< Maimaitawar Shari’a 34 >

1 Sai Musa ya hau Dutsen Nebo daga filayen Mowab, zuwa ƙwanƙolin Fisga, wanda yake ƙetare Yeriko. A can Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, daga Gileyad zuwa Dan,
Tad Mozus uzkāpa no Moaba klajumiem uz Nebus kalnu, Pizgas virsgalu, kas ir pret Jēriku, un Tas Kungs viņam rādīja visu Gileādas zemi līdz Danam,
2 da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,
Un visu Naftalus un Efraīma un Manasus zemi un visu Jūda zemi līdz pat jūrai,
3 da Negeb da dukan yankin Kwarin Yeriko, Birnin Dabino, har zuwa Zowar.
Un to dienvidu(Negebas) pusi un to klajumu, to palmu pilsētu, Jērikus leju, līdz Coārai.
4 Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, “Wannan ce ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, sa’ad da na ce, ‘Zan ba da ita ga zuriyarku.’ Na bar ka ka gani da idanunka, amma ba za ka haye zuwa cikinta ba.”
Un Tas Kungs sacīja uz viņu: “Šī ir tā zeme, ko Es Ābrahāmam, Īzakam un Jēkabam esmu zvērējis sacīdams: tavam dzimumam Es to došu; Es tev to esmu licis redzēt ar tavām acīm, bet tev nebūs uz turieni iet pāri.”
5 Nan fa, a ƙasar Mowab Musa bawan Ubangiji ya mutu, yadda Ubangiji ya faɗa.
Tā Mozus, Tā Kunga kalps, nomira Moaba zemē pēc Tā Kunga vārda.
6 Aka binne shi a Mowab, a kwarin kusa da Bet-Feyor, amma har wa yau babu wanda ya san inda kabarinsa yake.
Un Viņš to apraka ielejā, Moaba zemē, Bet Peoram pretī, un neviens viņa kapu nezin līdz šai dienai.
7 Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya mutu, duk da haka idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuwa bai ragu ba.
Un Mozus bija simts un divdesmit gadus vecs, kad viņš nomira. Viņa acis nebija palikušas tumšas un viņa spēks nebija zudis.
8 Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab kwana talatin, sai da lokacin kuka, da na makoki suka ƙare.
Un Israēla bērni apraudāja Mozu Moaba klajumos trīsdesmit dienas, tad tās gaudu un raudu dienas par Mozu beidzās.
9 To, Yoshuwa ɗan Nun ya cika da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Saboda haka Isra’ilawa suka saurare shi, suka kuma aikata abin da Ubangiji ya umarci Musa.
Un Jozuas, Nuna dēls, bija gudrības gara pilns, jo Mozus uz viņu bija uzlicis savas rokas, un Israēla bērni viņam klausīja un darīja, kā Tas Kungs Mozum bija pavēlējis.
10 Tun daga nan ba a sāke yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska,
Un tāds pravietis iekš Israēla vairs necēlās, kā Mozus, ko Tas Kungs būtu atzinis vaigu vaigā, -
11 wanda kuma ya yi dukan waɗannan alamu banmamaki da al’ajaban da Ubangiji ya aike shi yă yi a Masar, da a kan Fir’auna, da a kan dukan shugabanninsa, da kuma a kan dukan ƙasarsa.
Pēc visām tām zīmēm un tiem brīnumiem, ko darīt Tas Kungs viņu bija sūtījis uz Ēģiptes zemi pie Faraona un pie visiem viņa kalpiem un pie visas viņa zemes,
12 Gama babu wani wanda ya taɓa nuna iko mai ƙarfi, ko yă aikata ayyukan banrazana waɗanda Musa ya yi a gaban dukan Isra’ila.
Un pēc tās stiprās rokas un pēc visiem tiem lieliem un bijājamiem darbiem, ko Mozus darīja priekš visa Israēla acīm.

< Maimaitawar Shari’a 34 >