< Maimaitawar Shari’a 34 >

1 Sai Musa ya hau Dutsen Nebo daga filayen Mowab, zuwa ƙwanƙolin Fisga, wanda yake ƙetare Yeriko. A can Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, daga Gileyad zuwa Dan,
Dari dataran Moab, Musa kemudian naik ke puncak Pisga di gunung Nebo, di seberang Yeriko. Dari sana, TUHAN menunjukkan kepadanya seluruh negeri itu, yaitu daerah Gilead sampai kota Dan,
2 da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,
seluruh wilayah yang kelak dimiliki oleh suku Naftali, Efraim dan Manasye, serta wilayah yang terbentang sampai Laut Tengah, yang nantinya dimiliki oleh suku Yehuda,
3 da Negeb da dukan yankin Kwarin Yeriko, Birnin Dabino, har zuwa Zowar.
juga padang belantara Negeb di bagian selatan wilayah Yehuda, dan lembah Yordan yang terbentang dari Yeriko, kota pohon palem itu, sampai kota Zoar.
4 Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, “Wannan ce ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, sa’ad da na ce, ‘Zan ba da ita ga zuriyarku.’ Na bar ka ka gani da idanunka, amma ba za ka haye zuwa cikinta ba.”
Kata TUHAN kepada Musa, “Inilah negeri yang sudah Aku janjikan kepada Abraham, Isak, dan Yakub dengan berkata kepada mereka, ‘Aku akan memberikan negeri itu kepada keturunanmu.’ Sekarang Aku sudah mengizinkan kamu untuk melihatnya dari jauh, tetapi kamu tidak akan masuk ke sana.”
5 Nan fa, a ƙasar Mowab Musa bawan Ubangiji ya mutu, yadda Ubangiji ya faɗa.
Lalu Musa, hamba TUHAN itu, meninggal di negeri Moab, seperti yang sudah dikatakan TUHAN.
6 Aka binne shi a Mowab, a kwarin kusa da Bet-Feyor, amma har wa yau babu wanda ya san inda kabarinsa yake.
TUHAN menguburkan Musa di suatu lembah di Moab, di seberang kota Bet Peor, tetapi sampai hari penulisan kitab ini, tidak ada yang tahu letak kuburan Musa.
7 Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya mutu, duk da haka idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuwa bai ragu ba.
Musa berumur 120 tahun waktu dia meninggal. Saat itu tubuhnya masih kuat dan matanya tidak rabun.
8 Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab kwana talatin, sai da lokacin kuka, da na makoki suka ƙare.
Bangsa Israel meratapi dia di dataran Moab selama 30 hari, sesuai kebiasaan mereka.
9 To, Yoshuwa ɗan Nun ya cika da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Saboda haka Isra’ilawa suka saurare shi, suka kuma aikata abin da Ubangiji ya umarci Musa.
TUHAN memberi hikmat yang luar biasa kepada Yosua karena dia sudah ditunjuk oleh Musa menjadi penggantinya. Karena itu umat Israel menaati Yosua dan melakukan semua perintah TUHAN yang sudah disampaikan oleh Musa.
10 Tun daga nan ba a sāke yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska,
Sampai waktu penulisan kitab ini, tidak pernah ada lagi nabi yang seperti Musa di Israel, yang berulang kali berbicara langsung dengan TUHAN.
11 wanda kuma ya yi dukan waɗannan alamu banmamaki da al’ajaban da Ubangiji ya aike shi yă yi a Masar, da a kan Fir’auna, da a kan dukan shugabanninsa, da kuma a kan dukan ƙasarsa.
Tidak ada nabi lain yang melakukan berbagai keajaiban besar atas perintah TUHAN seperti yang dibuat Musa terhadap raja Mesir, para pejabatnya, dan seluruh negeri itu.
12 Gama babu wani wanda ya taɓa nuna iko mai ƙarfi, ko yă aikata ayyukan banrazana waɗanda Musa ya yi a gaban dukan Isra’ila.
Tidak ada lagi nabi yang kepadanya diberikan kuasa hebat untuk melakukan perbuatan-perbuatan dahsyat dan mengerikan seperti yang dilakukan Musa di hadapan semua orang Israel.

< Maimaitawar Shari’a 34 >