< Maimaitawar Shari’a 34 >

1 Sai Musa ya hau Dutsen Nebo daga filayen Mowab, zuwa ƙwanƙolin Fisga, wanda yake ƙetare Yeriko. A can Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, daga Gileyad zuwa Dan,
Moïse donc monta des plaines de Moab sur la montagne de Nébo au sommet de Phasga contre Jéricho; et le Seigneur lui montra toute la terre de Galaad jusqu’à Dan,
2 da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,
Tout Nephtali, la terre d’Ephraïm et de Manassé et toute la terre de Juda, jusqu’à la dernière mer;
3 da Negeb da dukan yankin Kwarin Yeriko, Birnin Dabino, har zuwa Zowar.
Et la partie australe, ainsi que l’étendue de la campagne de Jéricho ville des palmes jusqu’à Ségor.
4 Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, “Wannan ce ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, sa’ad da na ce, ‘Zan ba da ita ga zuriyarku.’ Na bar ka ka gani da idanunka, amma ba za ka haye zuwa cikinta ba.”
Et le Seigneur lui dit: Voici la terre au sujet de laquelle j’ai juré à Abraham, à Isaac et à Jacob, disant: C’est à ta postérité que je la donnerai. Tu l’as vue de tes yeux, et tu n’y passeras pas.
5 Nan fa, a ƙasar Mowab Musa bawan Ubangiji ya mutu, yadda Ubangiji ya faɗa.
Et Moïse, serviteur du Seigneur, mourut là dans la terre de Moab, le Seigneur l’ordonnant;
6 Aka binne shi a Mowab, a kwarin kusa da Bet-Feyor, amma har wa yau babu wanda ya san inda kabarinsa yake.
Et il l’ensevelit dans la vallée de la terre de Moab contre Phogor; et aucun homme n’a connu son sépulcre jusqu’au présent jour.
7 Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya mutu, duk da haka idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuwa bai ragu ba.
Moïse avait cent et vingt ans quand il mourut; son œil ne s’obscurcit pas, et ses dents ne furent pas ébranlées.
8 Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab kwana talatin, sai da lokacin kuka, da na makoki suka ƙare.
Les enfants d’Israël le pleurèrent dans les plaines de Moab durant trente jours: ainsi furent accomplis les jours du deuil de ceux qui pleuraient Moïse.
9 To, Yoshuwa ɗan Nun ya cika da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Saboda haka Isra’ilawa suka saurare shi, suka kuma aikata abin da Ubangiji ya umarci Musa.
Or, Josué, fils de Nun, fut rempli de l’Esprit de sagesse, parce que Moïse avait posé sur lui ses mains. Et les enfants d’Israël lui obéirent et ils firent comme avait ordonné le Seigneur à Moïse.
10 Tun daga nan ba a sāke yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska,
Et il ne s’éleva plus de prophète en Israël comme Moïse, que le Seigneur connût face à face,
11 wanda kuma ya yi dukan waɗannan alamu banmamaki da al’ajaban da Ubangiji ya aike shi yă yi a Masar, da a kan Fir’auna, da a kan dukan shugabanninsa, da kuma a kan dukan ƙasarsa.
À cause de tous les signes et de tous les prodiges qu’il l’envoya faire dans la terre d’Egypte contre Pharaon, contre ses serviteurs et contre toute sa terre,
12 Gama babu wani wanda ya taɓa nuna iko mai ƙarfi, ko yă aikata ayyukan banrazana waɗanda Musa ya yi a gaban dukan Isra’ila.
Et à cause de toute cette main forte, et de ces grandes merveilles que fit Moïse devant tout Israël.

< Maimaitawar Shari’a 34 >