< Maimaitawar Shari’a 34 >

1 Sai Musa ya hau Dutsen Nebo daga filayen Mowab, zuwa ƙwanƙolin Fisga, wanda yake ƙetare Yeriko. A can Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, daga Gileyad zuwa Dan,
Moïse monta des plaines de Moab au mont Nébo, au sommet du Pisga, qui est en face de Jéricho. Yahvé lui montra tout le pays de Galaad jusqu'à Dan,
2 da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,
tout Nephtali, le pays d'Éphraïm et de Manassé, et tout le pays de Juda, jusqu'à la mer Occidentale,
3 da Negeb da dukan yankin Kwarin Yeriko, Birnin Dabino, har zuwa Zowar.
et le sud, la plaine de la vallée de Jéricho, la ville des palmiers, jusqu'à Zoar.
4 Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, “Wannan ce ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, sa’ad da na ce, ‘Zan ba da ita ga zuriyarku.’ Na bar ka ka gani da idanunka, amma ba za ka haye zuwa cikinta ba.”
Yahvé lui dit: « Voici le pays que j'ai juré à Abraham, à Isaac et à Jacob, en disant: « Je le donnerai à ta postérité ». Je te l'ai fait voir de tes yeux, mais tu n'y passeras pas. »
5 Nan fa, a ƙasar Mowab Musa bawan Ubangiji ya mutu, yadda Ubangiji ya faɗa.
Et Moïse, serviteur de Yahvé, mourut là, au pays de Moab, selon la parole de Yahvé.
6 Aka binne shi a Mowab, a kwarin kusa da Bet-Feyor, amma har wa yau babu wanda ya san inda kabarinsa yake.
Il fut enterré dans la vallée du pays de Moab, en face de Beth Peor, mais personne ne sait encore aujourd'hui où se trouve sa tombe.
7 Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya mutu, duk da haka idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuwa bai ragu ba.
Moïse était âgé de cent vingt ans lorsqu'il mourut. Son œil ne s'était pas affaibli, et sa force n'avait pas disparu.
8 Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab kwana talatin, sai da lokacin kuka, da na makoki suka ƙare.
Les enfants d'Israël pleurèrent Moïse dans les plaines de Moab pendant trente jours, jusqu'à ce que les jours de deuil de Moïse fussent terminés.
9 To, Yoshuwa ɗan Nun ya cika da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Saboda haka Isra’ilawa suka saurare shi, suka kuma aikata abin da Ubangiji ya umarci Musa.
Josué, fils de Nun, était rempli de l'esprit de sagesse, car Moïse avait posé ses mains sur lui. Les enfants d'Israël l'écoutèrent et firent ce que l'Éternel avait ordonné à Moïse.
10 Tun daga nan ba a sāke yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska,
Depuis lors, il n'a pas paru en Israël de prophète semblable à Moïse, que l'Éternel a connu face à face,
11 wanda kuma ya yi dukan waɗannan alamu banmamaki da al’ajaban da Ubangiji ya aike shi yă yi a Masar, da a kan Fir’auna, da a kan dukan shugabanninsa, da kuma a kan dukan ƙasarsa.
par tous les signes et les prodiges que l'Éternel l'a envoyé faire au pays d'Égypte, à Pharaon, à tous ses serviteurs et à tout son pays,
12 Gama babu wani wanda ya taɓa nuna iko mai ƙarfi, ko yă aikata ayyukan banrazana waɗanda Musa ya yi a gaban dukan Isra’ila.
par toute la puissance de sa main et par toutes les merveilles qu'il a faites aux yeux de tout Israël.

< Maimaitawar Shari’a 34 >