< Maimaitawar Shari’a 34 >
1 Sai Musa ya hau Dutsen Nebo daga filayen Mowab, zuwa ƙwanƙolin Fisga, wanda yake ƙetare Yeriko. A can Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, daga Gileyad zuwa Dan,
And Moses goeth up from the plains of Moab unto mount Nebo, the top of Pisgah, which [is] on the front of Jericho, and Jehovah sheweth him all the land — Gilead unto Dan,
2 da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,
and all Naphtali, and the land of Ephraim, and Manasseh, and all the land of Judah unto the further sea,
3 da Negeb da dukan yankin Kwarin Yeriko, Birnin Dabino, har zuwa Zowar.
and the south, and the circuit of the valley of Jericho, the city of palms, unto Zoar.
4 Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, “Wannan ce ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, sa’ad da na ce, ‘Zan ba da ita ga zuriyarku.’ Na bar ka ka gani da idanunka, amma ba za ka haye zuwa cikinta ba.”
And Jehovah saith unto him, 'This [is] the land which I have sworn to Abraham, to Isaac, and to Jacob, saying, To thy seed I give it; I have caused thee to see with thine eyes, and thither thou dost not pass over.'
5 Nan fa, a ƙasar Mowab Musa bawan Ubangiji ya mutu, yadda Ubangiji ya faɗa.
And Moses, servant of the Lord, dieth there, in the land of Moab, according to the command of Jehovah;
6 Aka binne shi a Mowab, a kwarin kusa da Bet-Feyor, amma har wa yau babu wanda ya san inda kabarinsa yake.
and He burieth him in a valley in the land of Moab, over-against Beth-Peor, and no man hath known his burying place unto this day.
7 Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya mutu, duk da haka idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuwa bai ragu ba.
And Moses [is] a son of a hundred and twenty years when he dieth; his eye hath not become dim, nor hath his moisture fled.
8 Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab kwana talatin, sai da lokacin kuka, da na makoki suka ƙare.
And the sons of Israel bewail Moses in the plains of Moab thirty days; and the days of weeping [and] mourning for Moses are completed.
9 To, Yoshuwa ɗan Nun ya cika da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Saboda haka Isra’ilawa suka saurare shi, suka kuma aikata abin da Ubangiji ya umarci Musa.
And Joshua son of Nun is full of the spirit of wisdom, for Moses had laid his hands upon him, and the sons of Israel hearken unto him, and do as Jehovah commanded Moses.
10 Tun daga nan ba a sāke yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska,
And there hath not arisen a prophet any more in Israel like Moses, whom Jehovah hath known face unto face,
11 wanda kuma ya yi dukan waɗannan alamu banmamaki da al’ajaban da Ubangiji ya aike shi yă yi a Masar, da a kan Fir’auna, da a kan dukan shugabanninsa, da kuma a kan dukan ƙasarsa.
in reference to all the signs and the wonders which Jehovah sent him to do in the land of Egypt, to Pharaoh, and to all his servants, and to all his land,
12 Gama babu wani wanda ya taɓa nuna iko mai ƙarfi, ko yă aikata ayyukan banrazana waɗanda Musa ya yi a gaban dukan Isra’ila.
and in reference to all the strong hand, and to all the great fear which Moses did before the eyes of all Israel.