< Maimaitawar Shari’a 34 >
1 Sai Musa ya hau Dutsen Nebo daga filayen Mowab, zuwa ƙwanƙolin Fisga, wanda yake ƙetare Yeriko. A can Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, daga Gileyad zuwa Dan,
So then Moses went up, from the waste plains of Moab into Mount Nebo, the head of Pisgah, which is over against Jericho, —and Yahweh showed him all the land—even Gilead as far as Dan;
2 da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,
and all Naphtali, and the land of Ephraim and Manasseh, —and all the land of Judah, as far as the hinder sea;
3 da Negeb da dukan yankin Kwarin Yeriko, Birnin Dabino, har zuwa Zowar.
and the South, —and the circuit of the valley of Jericho, the city of palm trees as far as Zoar.
4 Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, “Wannan ce ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, sa’ad da na ce, ‘Zan ba da ita ga zuriyarku.’ Na bar ka ka gani da idanunka, amma ba za ka haye zuwa cikinta ba.”
And Yahweh said unto him—This, is the land which I sware to Abraham, to Isaac, and to Jacob, saying, Unto thy seed, will I give it. I have let thee see with thine own eyes, But thither, shalt thou not pass over.
5 Nan fa, a ƙasar Mowab Musa bawan Ubangiji ya mutu, yadda Ubangiji ya faɗa.
So Moses, the servant of Yahweh, died there, in the land of Moab, at the bidding of Yahweh;
6 Aka binne shi a Mowab, a kwarin kusa da Bet-Feyor, amma har wa yau babu wanda ya san inda kabarinsa yake.
and he buried him, in a valley in the land of Moab, over against Beth-peor, —but no man hath known his burying-place, until this day.
7 Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya mutu, duk da haka idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuwa bai ragu ba.
Now, Moses, was a hundred and twenty years old, when he died, —his eye had not dimmed, nor had his freshness fled.
8 Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab kwana talatin, sai da lokacin kuka, da na makoki suka ƙare.
And the sons of Israel bewailed Moses in the waste plains of Moab thirty days, —then were completed the wailing-days of the mourning for Moses.
9 To, Yoshuwa ɗan Nun ya cika da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Saboda haka Isra’ilawa suka saurare shi, suka kuma aikata abin da Ubangiji ya umarci Musa.
But, Joshua, son of Nun, was full of the spirit of wisdom, for Moses had laid his hands upon him, —so the sons of Israel hearkened unto him, and did, as Yahweh commanded Moses.
10 Tun daga nan ba a sāke yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska,
And there arose not a prophet any more in Israel, like unto Moses, —whom Yahweh acknowledged, face to face;
11 wanda kuma ya yi dukan waɗannan alamu banmamaki da al’ajaban da Ubangiji ya aike shi yă yi a Masar, da a kan Fir’auna, da a kan dukan shugabanninsa, da kuma a kan dukan ƙasarsa.
by all the signs and the wonders which Yahweh sent him to do in the land of Egypt, —unto Pharaoh and unto all his servants and unto all his land;
12 Gama babu wani wanda ya taɓa nuna iko mai ƙarfi, ko yă aikata ayyukan banrazana waɗanda Musa ya yi a gaban dukan Isra’ila.
and by all the firm hand, and by all the great terror which Moses wrought in the sight of all Israel.