< Maimaitawar Shari’a 34 >

1 Sai Musa ya hau Dutsen Nebo daga filayen Mowab, zuwa ƙwanƙolin Fisga, wanda yake ƙetare Yeriko. A can Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, daga Gileyad zuwa Dan,
Then Moses went from the plaine of Moab vp into mount Nebo vnto the top of Pisgah that is ouer against Iericho: and the Lord shewed him all the land of Gilead, vnto Dan,
2 da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,
And all Naphtali and the land of Ephraim and Manasseh, and all the land of Iudah, vnto the vtmost sea:
3 da Negeb da dukan yankin Kwarin Yeriko, Birnin Dabino, har zuwa Zowar.
And the South, and the plaine of the valley of Iericho, the citie of palmetrees, vnto Zoar.
4 Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, “Wannan ce ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, sa’ad da na ce, ‘Zan ba da ita ga zuriyarku.’ Na bar ka ka gani da idanunka, amma ba za ka haye zuwa cikinta ba.”
And the Lord said vnto him, This is the lande which I sware vnto Abraham, to Izhak and to Iaacob saying, I will giue it vnto thy seede: I haue caused thee to see it with thine eyes, but thou shalt not goe ouer thither.
5 Nan fa, a ƙasar Mowab Musa bawan Ubangiji ya mutu, yadda Ubangiji ya faɗa.
So Moses the seruant of the Lord dyed there in the land of Moab, according to the worde of the Lord.
6 Aka binne shi a Mowab, a kwarin kusa da Bet-Feyor, amma har wa yau babu wanda ya san inda kabarinsa yake.
And hee buried him in a valley in the land of Moab ouer against Beth-peor, but no man knoweth of his sepulchre vnto this day.
7 Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya mutu, duk da haka idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuwa bai ragu ba.
Moses was nowe an hundreth and twentie yeere olde when hee died, his eye was not dimme, nor his naturall force abated.
8 Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab kwana talatin, sai da lokacin kuka, da na makoki suka ƙare.
And the children of Israel wept for Moses in the plaine of Moab thirtie dayes: so the dayes of weeping and mourning for Moses were ended.
9 To, Yoshuwa ɗan Nun ya cika da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Saboda haka Isra’ilawa suka saurare shi, suka kuma aikata abin da Ubangiji ya umarci Musa.
And Ioshua the sonne of Nun was full of ye spirit of wisedome: for Moses had put his hands vpon him. And the children of Israel were obedient vnto him, and did as the Lord had commanded Moses.
10 Tun daga nan ba a sāke yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska,
But there arose not a Prophet since in Israel like vnto Moses (whome the Lord knew face to face)
11 wanda kuma ya yi dukan waɗannan alamu banmamaki da al’ajaban da Ubangiji ya aike shi yă yi a Masar, da a kan Fir’auna, da a kan dukan shugabanninsa, da kuma a kan dukan ƙasarsa.
In all ye miracles and wonders which ye Lord sent him to do in ye land of Egypt before Pharaoh and before all his seruantes, and before al his land,
12 Gama babu wani wanda ya taɓa nuna iko mai ƙarfi, ko yă aikata ayyukan banrazana waɗanda Musa ya yi a gaban dukan Isra’ila.
And in all that mightie hand and all that great feare, which Moses wrought in the sight of all Israel.

< Maimaitawar Shari’a 34 >