< Maimaitawar Shari’a 34 >

1 Sai Musa ya hau Dutsen Nebo daga filayen Mowab, zuwa ƙwanƙolin Fisga, wanda yake ƙetare Yeriko. A can Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, daga Gileyad zuwa Dan,
And Moses went up from the table-lands of Moab to Mount Nebo, to the top of Pisgah which is facing Jericho. And the Lord let him see all the land, the land of Gilead as far as Dan;
2 da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,
And all Naphtali and the land of Ephraim and Manasseh, and all the land of Judah, as far as the Great Sea of the west;
3 da Negeb da dukan yankin Kwarin Yeriko, Birnin Dabino, har zuwa Zowar.
And the South, and the circle of the valley of Jericho, the town of palm-trees, as far as Zoar.
4 Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, “Wannan ce ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, sa’ad da na ce, ‘Zan ba da ita ga zuriyarku.’ Na bar ka ka gani da idanunka, amma ba za ka haye zuwa cikinta ba.”
And the Lord said to him, This is the land about which I made an oath to Abraham, Isaac, and Jacob, saying, I will give it to your seed: now I have let you see it with your eyes, but you will not go in there.
5 Nan fa, a ƙasar Mowab Musa bawan Ubangiji ya mutu, yadda Ubangiji ya faɗa.
So death came to Moses, the servant of the Lord, there in the land of Moab, as the Lord had said.
6 Aka binne shi a Mowab, a kwarin kusa da Bet-Feyor, amma har wa yau babu wanda ya san inda kabarinsa yake.
And the Lord put him to rest in the valley in the land of Moab opposite Beth-peor: but no man has knowledge of his resting-place to this day.
7 Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya mutu, duk da haka idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuwa bai ragu ba.
And Moses at his death was a hundred and twenty years old: his eye had not become clouded, or his natural force become feeble.
8 Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab kwana talatin, sai da lokacin kuka, da na makoki suka ƙare.
For thirty days the children of Israel were weeping for Moses in the table-lands of Moab, till the days of weeping and sorrow for Moses were ended.
9 To, Yoshuwa ɗan Nun ya cika da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Saboda haka Isra’ilawa suka saurare shi, suka kuma aikata abin da Ubangiji ya umarci Musa.
And Joshua, the son of Nun, was full of the spirit of wisdom; for Moses had put his hands on him: and the children of Israel gave ear to him, and did as the Lord had given orders to Moses.
10 Tun daga nan ba a sāke yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska,
There has never been another prophet in Israel like Moses, whom the Lord had knowledge of face to face;
11 wanda kuma ya yi dukan waɗannan alamu banmamaki da al’ajaban da Ubangiji ya aike shi yă yi a Masar, da a kan Fir’auna, da a kan dukan shugabanninsa, da kuma a kan dukan ƙasarsa.
In all the signs and wonders which the Lord sent him to do in the land of Egypt, to Pharaoh and to all his servants and all his land;
12 Gama babu wani wanda ya taɓa nuna iko mai ƙarfi, ko yă aikata ayyukan banrazana waɗanda Musa ya yi a gaban dukan Isra’ila.
And in all the acts of power and fear which Moses did before the eyes of all Israel.

< Maimaitawar Shari’a 34 >