< Maimaitawar Shari’a 33 >

1 Wannan ita ce albarkar da Musa mutumin Allah ya furta a kan Isra’ilawa, kafin yă rasu.
Dette er den velsignelse som Moses, den Guds mann, lyste over Israels barn før sin død.
2 Ya ce, “Ubangiji ya zo daga Sinai ya haskaka a bisansu daga Seyir; ya haskaka daga Dutsen Faran. Ya zo tare da dubban tsarkakansa daga kudu, daga gangara dutsensa.
Han sa: Herren kom fra Sinai, han steg op for dem fra Se'ir; han strålte frem fra Parans fjell og kom fra hellige titusener; ved hans høire hånd lyste lovens ild for dem.
3 Tabbatacce kai ne wanda yake ƙaunar mutane; dukan tsarkaka suna a hannunka. A ƙafafunka, duk suka rusuna, daga wurinka kuma suka karɓi umarni,
Ja, han elsker sitt folk; alle dine hellige er i din hånd; de ligger for din fot, de tar imot dine ord.
4 dokar Musa ta ba mu dokoki, mallakar taron Yaƙub.
En lov gav Moses oss, en arvedel for Jakobs menighet.
5 Shi ne sarki a bisa Yeshurun sa’ad da shugabannin mutane suka taru, tare da kabilan Isra’ila.
Og han blev konge i Jesurun, da folkets høvdinger samlet sig, Israels stammer alle sammen.
6 “Bari Ruben yă rayu, kada yă mutu, kada mutanensa su zama kaɗan.”
Måtte Ruben leve og aldri dø, men hans menn bli få i tall!
7 Ya kuma faɗa wannan game da Yahuda, “Ka ji, ya Ubangiji, kukan Yahuda; ka kawo shi wurin mutanensa. Da hannuwansa ya kāre kansa. Ka taimake shi a kan maƙiyansa!”
Og dette sa han om Juda: Hør, Herre, Judas røst, og før ham hjem til sitt folk! Med sine hender strider han for det, og du skal være hans hjelp mot hans fiender.
8 Game da Lawi ya ce, “Tummim da Urim na mutumin da ka nuna masa tagomashi ne. Ka gwada shi a Massa; ka yi faɗa da shi a ruwan Meriba.
Og om Levi sa han: Dine tummim og urim hører din fromme mann til, han som du fristet ved Massa, som du trettet med ved Meribas vann,
9 Ya yi zancen mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, ‘Ban kula da su ba.’ Bai gane da’yan’uwansa ba, ko yă yarda da’ya’yansa, amma ya kiyaye maganarka ya tsare alkawarinka.
han som sa om sin far og sin mor: Jeg ser dem ikke, og som ikke kjentes ved sine brødre og ikke visste av sine barn, fordi han tok vare på ditt ord og aktet vel på din pakt.
10 Ya koyar da farillanka ga Yaƙub, dokarka kuma ga Isra’ila. Ya miƙa turare a gabanka da kuma hadaya ta ƙonawa ɗungum a kan bagadenka.
Han skal lære Jakob dine bud og Israel din lov, han skal legge røkelse for ditt ansikt og heloffer på ditt alter.
11 Ka albarkaci ɗaukan dabarunsa, ya Ubangiji, ka kuma ji daɗin aikin hannuwansa. Ka murƙushe kwankwaso waɗanda suka tayar masa; ka bugi abokan gābansa har sai ba su ƙara tashi ba.”
Velsign, Herre, hans kraft, og la hans henders gjerning tekkes dig! Knus lendene på hans motstandere og dem som hater ham, så de ikke reiser sig mere!
12 Game da Benyamin ya ce, “Bari ƙaunataccen Ubangiji yă zauna lafiya kusa da shi, gama yana tsare shi dukan yini, wanda kuma Ubangiji yake ƙauna yana zama a tsakanin kafaɗunsa.”
Om Benjamin sa han: Herrens elskede er han, trygt bor han hos ham; hele dagen holder han sin hånd over ham - han hviler mellem hans skuldrer.
13 Game da Yusuf ya ce, “Bari Ubangiji yă albarkaci ƙasarsa da raɓa mai daraja daga sama a bisa da kuma zurfin ruwan da suke kwance a ƙarƙashi;
Og om Josef sa han: Velsignet av Herren være hans land med himmelens ypperste gaver, med dugg og med vann fra det store dyp der nede,
14 da abubuwa masu kyau da rana take kawo, da kuma abubuwa mafi kyau da wata zai iya haifar;
med det ypperste av det som solen fostrer, med det ypperste av det som måneskiftene driver frem,
15 da zaɓaɓɓun kyautai na daɗaɗɗun duwatsu, da kyawawan amfani na madawwaman tuddai.
med det herligste fra de eldgamle fjell og det ypperste fra de evige hauger,
16 Tare da kyautai mafi kyau na duniya da cikarta, da tagomashi na wanda yake zama a ƙaramin itace mai ƙonewa. Bari duk waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin sarki a cikin’yan’uwansa.
med det ypperste av jorden og dens fylde og med nåde fra ham som bodde i tornebusken; det komme over Josefs hode, over hans isse som er fyrste blandt sine brødre!
17 Cikin daraja yana yi kamar ɗan fari na bijimi; ƙahoninsa ƙahonin ɓauna ne. Tare da su zai tukwiyi al’ummai, har ma da waɗanda suke ƙarshen duniya. Haka dubu dubban Efraim suke; haka dubban Manasse suke.”
Herlig er den førstefødte av hans okser, og hans horn er som villoksens horn; med dem stanger han alle folkene like til jordens ender; det er Efra'ims titusener, det er Manasses tusener.
18 Game da Zebulun ya ce, “Ka yi farin ciki, Zebulun, a fitowarka, kai kuma Issakar, a cikin tentunanka.
Og om Sebulon sa han: Gled dig, Sebulon, i din utferd, og du, Issakar, i dine telt!
19 Za su kira mutane zuwa dutse, a can za su miƙa hadayun adalci; za su yi biki a yalwan tekuna, a dukiyoyin da aka ɓoye a cikin yashi.”
Folkeslag kaller de til sitt fjell; der ofrer de rettferdighets offere; for havets overflod og sandens skjulte skatter suger de inn.
20 Game da Gad ya ce, “Mai albarka ne wanda ya fadada mazaunin Gad! Gad yana zama a can kamar zaki, yana yayyage a hannu da kai.
Og om Gad sa han: Lovet være han som gir Gad vidt rum! Som en løvinne har han lagt sig ned, og han sønderriver både arm og isse.
21 Ya zaɓi ƙasa mafi kyau wa kansa; aka ajiye masa rabon shugaba. Sa’ad da shugabannin mutane suka taru, ya aikata adalcin Ubangiji da kuma hukuncinsa game da Isra’ila.”
Han utså sig den første lodd, for der er den del gjemt som lovgiveren har tiltenkt ham; og så drog han frem foran folket; det som var rett for Herren, det som han hadde fastsatt, gjorde han, sammen med Israel.
22 Game da Dan ya ce, “Dan ɗan zaki ne, yana tsalle daga Bashan.”
Og om Dan sa han: Dan er en løveunge som springer frem fra Basan.
23 Game da Naftali ya ce, “Naftali ƙosasshe ne da tagomashin Ubangiji, ya kuma cika albarkarsa; zai gāji gefen kudu zuwa tafki.”
Og om Naftali sa han: Naftali, mettet med nåde og fylt med Herrens velsignelse - Vesten og Syden ta han i eie!
24 Game da Asher ya ce, “Mafi albarka na’ya’yan, shi ne Asher; bari yă sami tagomashi daga’yan’uwansa, bari kuma yă wanke ƙafafunsa a cikin mai.
Og om Aser sa han: Velsignet fremfor sønner være Aser! han være den kjæreste blandt sine brødre og dyppe i olje sin fot!
25 Madogaran ƙofofinka za su zama ƙarfe da tagulla, ƙarfinka kuma zai zama daidai da kwanakinka.
Av jern og kobber være din lås, og din hvile så lang som dine dager!
26 “Babu wani kamar Allah na Yeshurun, wanda yake hawa a bisa sammai don yă taimake ka a kan gizagizai kuma a cikin darajarsa.
Det er ingen som Gud, Jesurun! - Han farer frem over himmelen med hjelp for dig, og i sin høihet på skyene.
27 Allah madawwami shi ne mafakarka, a ƙarƙashina kuma madawwamin hannuwa ne. Zai kore abokin gābanka a gabanka, yana cewa, ‘Ka hallaka shi!’
En bolig er den eldgamle Gud, og her nede er evige armer; han driver fienden bort for dig og sier: Rydd ut!
28 Haka Isra’ila zai zauna lafiya shi kaɗai; zuriyar Yaƙub a tsare a ƙasar hatsi da sabon ruwan inabi, inda sammai za su zuba raɓa.
Og Israel bor trygt for sig selv, Jakobs øie er vendt mot et land med korn og most, ja, hans himmel drypper av dugg.
29 Kai mai albarka ne, ya Isra’ila! Wane ne yake kamar ka, mutanen da Ubangiji ya ceta? Shi ne mafakarka da mai taimakonka da kuma takobinka mai ɗaukaka. Abokan gābanka za su zo neman jinƙai a gabanka, za ka kuwa tattake masujadansu.”
Salig er du, Israel! Hvem er som du, et folk som har sin frelse i Herren, ditt hjelpende skjold og ditt høie sverd! Dine fiender hykler for dig, mens du skrider frem over deres høider.

< Maimaitawar Shari’a 33 >