< Maimaitawar Shari’a 33 >
1 Wannan ita ce albarkar da Musa mutumin Allah ya furta a kan Isra’ilawa, kafin yă rasu.
This is the blessing with which Moses the man of God blessed the people of Israel before his death.
2 Ya ce, “Ubangiji ya zo daga Sinai ya haskaka a bisansu daga Seyir; ya haskaka daga Dutsen Faran. Ya zo tare da dubban tsarkakansa daga kudu, daga gangara dutsensa.
He said: Yahweh came from Sinai and rose from Seir upon them. He shined out from Mount Paran, and he came with ten thousands of holy ones. In his right hand were flashes of lightning.
3 Tabbatacce kai ne wanda yake ƙaunar mutane; dukan tsarkaka suna a hannunka. A ƙafafunka, duk suka rusuna, daga wurinka kuma suka karɓi umarni,
Indeed, he loves the peoples; all his holy ones are in your hand, and they bowed down at your feet; they received your words.
4 dokar Musa ta ba mu dokoki, mallakar taron Yaƙub.
Moses commanded us a law, an inheritance for the assembly of Jacob.
5 Shi ne sarki a bisa Yeshurun sa’ad da shugabannin mutane suka taru, tare da kabilan Isra’ila.
Then there was a king in Jeshurun, when the heads of the people had gathered, all the tribes of Israel together.
6 “Bari Ruben yă rayu, kada yă mutu, kada mutanensa su zama kaɗan.”
Let Reuben live and not die, but may his men be few.
7 Ya kuma faɗa wannan game da Yahuda, “Ka ji, ya Ubangiji, kukan Yahuda; ka kawo shi wurin mutanensa. Da hannuwansa ya kāre kansa. Ka taimake shi a kan maƙiyansa!”
This is the blessing for Judah. Moses said: Listen, Yahweh, to the voice of Judah, and bring him to his people again. Fight for him; be a help against his enemies.
8 Game da Lawi ya ce, “Tummim da Urim na mutumin da ka nuna masa tagomashi ne. Ka gwada shi a Massa; ka yi faɗa da shi a ruwan Meriba.
About Levi, Moses said: Your Thummim and your Urim belong your loyal one, the one whom you tested at Massah, with whom you struggled at the waters of Meribah.
9 Ya yi zancen mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, ‘Ban kula da su ba.’ Bai gane da’yan’uwansa ba, ko yă yarda da’ya’yansa, amma ya kiyaye maganarka ya tsare alkawarinka.
The man who said about his father and mother, “I have not seen them.” Neither did he acknowledge his brothers, nor did he take account of his own children. For he guarded your word and kept your covenant.
10 Ya koyar da farillanka ga Yaƙub, dokarka kuma ga Isra’ila. Ya miƙa turare a gabanka da kuma hadaya ta ƙonawa ɗungum a kan bagadenka.
He teaches Jacob your decrees and Israel your law. He will put incense before you and whole burnt offerings on your altar.
11 Ka albarkaci ɗaukan dabarunsa, ya Ubangiji, ka kuma ji daɗin aikin hannuwansa. Ka murƙushe kwankwaso waɗanda suka tayar masa; ka bugi abokan gābansa har sai ba su ƙara tashi ba.”
Bless, Yahweh, his possessions, and accept the work of his hands. Shatter the loins of those who rise up against him, and those of the people who hate him, so that they do not rise up again.
12 Game da Benyamin ya ce, “Bari ƙaunataccen Ubangiji yă zauna lafiya kusa da shi, gama yana tsare shi dukan yini, wanda kuma Ubangiji yake ƙauna yana zama a tsakanin kafaɗunsa.”
About Benjamin, Moses said: The one loved by Yahweh lives in security beside him; Yahweh shields him all the day long, and he lives between Yahweh's arms.
13 Game da Yusuf ya ce, “Bari Ubangiji yă albarkaci ƙasarsa da raɓa mai daraja daga sama a bisa da kuma zurfin ruwan da suke kwance a ƙarƙashi;
About Joseph, Moses said: May his land be blessed by Yahweh with the precious things of heaven, with the dew, and with the deep that lies beneath.
14 da abubuwa masu kyau da rana take kawo, da kuma abubuwa mafi kyau da wata zai iya haifar;
May his land be blessed with the precious things of the harvest of the sun, with the precious things of the produce of the months,
15 da zaɓaɓɓun kyautai na daɗaɗɗun duwatsu, da kyawawan amfani na madawwaman tuddai.
with the finest things of the ancient mountains, and with the precious things of the everlasting hills.
16 Tare da kyautai mafi kyau na duniya da cikarta, da tagomashi na wanda yake zama a ƙaramin itace mai ƙonewa. Bari duk waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin sarki a cikin’yan’uwansa.
May his land be blessed with the precious things of the earth and its abundance, and with the good will of him who was in the bush. Let the blessing come on the head of Joseph, and on the top of the head of him who was prince over his brothers.
17 Cikin daraja yana yi kamar ɗan fari na bijimi; ƙahoninsa ƙahonin ɓauna ne. Tare da su zai tukwiyi al’ummai, har ma da waɗanda suke ƙarshen duniya. Haka dubu dubban Efraim suke; haka dubban Manasse suke.”
The firstborn of an ox, majestic is he, and his horns are the horns of a wild ox. With them he will push the peoples, all of them, to the ends of the earth. These are the ten thousands of Ephraim; these are the thousands of Manasseh.
18 Game da Zebulun ya ce, “Ka yi farin ciki, Zebulun, a fitowarka, kai kuma Issakar, a cikin tentunanka.
About Zebulun, Moses said: Rejoice, Zebulun, in your going out, and you, Issachar, in your tents.
19 Za su kira mutane zuwa dutse, a can za su miƙa hadayun adalci; za su yi biki a yalwan tekuna, a dukiyoyin da aka ɓoye a cikin yashi.”
They will call the peoples to the mountains. There will they offer sacrifices of righteousness. For they will suck the abundance of the seas, and from the sand on the seashore.
20 Game da Gad ya ce, “Mai albarka ne wanda ya fadada mazaunin Gad! Gad yana zama a can kamar zaki, yana yayyage a hannu da kai.
About Gad, Moses said: Blessed be he who enlarges Gad. He will live there like a lioness, and he will tear off an arm or a head.
21 Ya zaɓi ƙasa mafi kyau wa kansa; aka ajiye masa rabon shugaba. Sa’ad da shugabannin mutane suka taru, ya aikata adalcin Ubangiji da kuma hukuncinsa game da Isra’ila.”
He provided the best part for himself, for there was the leader's portion of land reserved. He came with the heads of the people. He carried out the justice of Yahweh and his decrees with Israel.
22 Game da Dan ya ce, “Dan ɗan zaki ne, yana tsalle daga Bashan.”
About Dan, Moses said: Dan is a lion cub that leaps out from Bashan.
23 Game da Naftali ya ce, “Naftali ƙosasshe ne da tagomashin Ubangiji, ya kuma cika albarkarsa; zai gāji gefen kudu zuwa tafki.”
About Naphtali, Moses said: Naphtali, satisfied with favor, and full of the blessing of Yahweh, take possession of the land to the west and south.
24 Game da Asher ya ce, “Mafi albarka na’ya’yan, shi ne Asher; bari yă sami tagomashi daga’yan’uwansa, bari kuma yă wanke ƙafafunsa a cikin mai.
About Asher, Moses said: Blessed be Asher more than the other sons; let him be acceptable to his brothers, and let him dip his foot in olive oil.
25 Madogaran ƙofofinka za su zama ƙarfe da tagulla, ƙarfinka kuma zai zama daidai da kwanakinka.
May your city bars be iron and bronze; as long as will be your days, so long will your security be.
26 “Babu wani kamar Allah na Yeshurun, wanda yake hawa a bisa sammai don yă taimake ka a kan gizagizai kuma a cikin darajarsa.
There is no one like God, Jeshurun—the upright one, who rides through the heavens to your help, and in his majesty on the clouds.
27 Allah madawwami shi ne mafakarka, a ƙarƙashina kuma madawwamin hannuwa ne. Zai kore abokin gābanka a gabanka, yana cewa, ‘Ka hallaka shi!’
The eternal God is a refuge, and underneath are the everlasting arms. He thrust out the enemy from before you, and he said, “Destroy!”
28 Haka Isra’ila zai zauna lafiya shi kaɗai; zuriyar Yaƙub a tsare a ƙasar hatsi da sabon ruwan inabi, inda sammai za su zuba raɓa.
Israel dwelt in safety. Jacob's spring was secure in a land of grain and new wine; indeed, let his heavens drop dew on him.
29 Kai mai albarka ne, ya Isra’ila! Wane ne yake kamar ka, mutanen da Ubangiji ya ceta? Shi ne mafakarka da mai taimakonka da kuma takobinka mai ɗaukaka. Abokan gābanka za su zo neman jinƙai a gabanka, za ka kuwa tattake masujadansu.”
Your blessings are many, Israel! Who is like you, a people saved by Yahweh, the shield of your help, and the sword of your majesty? Your enemies will come trembling to you; you will trample down their high places.