< Maimaitawar Shari’a 33 >
1 Wannan ita ce albarkar da Musa mutumin Allah ya furta a kan Isra’ilawa, kafin yă rasu.
The following is the blessing that Moses the man of God gave to the Israelites before he died.
2 Ya ce, “Ubangiji ya zo daga Sinai ya haskaka a bisansu daga Seyir; ya haskaka daga Dutsen Faran. Ya zo tare da dubban tsarkakansa daga kudu, daga gangara dutsensa.
He said, The Lord came from Mount Sinai and shone on us from Mount Seir; he blazed out from Mount Paran coming with ten thousand of holy ones, holding flaming fire at his right hand.
3 Tabbatacce kai ne wanda yake ƙaunar mutane; dukan tsarkaka suna a hannunka. A ƙafafunka, duk suka rusuna, daga wurinka kuma suka karɓi umarni,
How much you love the people; you hold all the holy ones in your hand. They sit down at your feet to listen to your words:
4 dokar Musa ta ba mu dokoki, mallakar taron Yaƙub.
the law that Moses delivered to us that belongs to all the Israelites.
5 Shi ne sarki a bisa Yeshurun sa’ad da shugabannin mutane suka taru, tare da kabilan Isra’ila.
The Lord became King in Israel when the people's leaders gathered, when the tribes of Israel assembled.
6 “Bari Ruben yă rayu, kada yă mutu, kada mutanensa su zama kaɗan.”
To Reuben he said, “May he live and not die, but may he only have a few men.”
7 Ya kuma faɗa wannan game da Yahuda, “Ka ji, ya Ubangiji, kukan Yahuda; ka kawo shi wurin mutanensa. Da hannuwansa ya kāre kansa. Ka taimake shi a kan maƙiyansa!”
To Judah he said: “Lord, please hear the cry of Judah and reunite him with his people. Even though he fights for himself, may you help him against his enemies.”
8 Game da Lawi ya ce, “Tummim da Urim na mutumin da ka nuna masa tagomashi ne. Ka gwada shi a Massa; ka yi faɗa da shi a ruwan Meriba.
To Levi he said: “Your Thummim were given to Levi and your Urim to those dedicated to God, the ones you tested at Massah and argued with at the waters of Meribah.
9 Ya yi zancen mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, ‘Ban kula da su ba.’ Bai gane da’yan’uwansa ba, ko yă yarda da’ya’yansa, amma ya kiyaye maganarka ya tsare alkawarinka.
Levi said that he didn't pay attention to his father and mother, that he didn't acknowledge his brothers, and that he didn't recognize his children. The Levites did what you said and kept your agreement.
10 Ya koyar da farillanka ga Yaƙub, dokarka kuma ga Isra’ila. Ya miƙa turare a gabanka da kuma hadaya ta ƙonawa ɗungum a kan bagadenka.
They will teach your regulations to Jacob and your law to Israel. They will place incense before you, and sacrifice whole burnt offerings on your altar.
11 Ka albarkaci ɗaukan dabarunsa, ya Ubangiji, ka kuma ji daɗin aikin hannuwansa. Ka murƙushe kwankwaso waɗanda suka tayar masa; ka bugi abokan gābansa har sai ba su ƙara tashi ba.”
Lord, please bless what they have, and accept their service for you. Destroy those who attack them; make sure their enemies never rise again.”
12 Game da Benyamin ya ce, “Bari ƙaunataccen Ubangiji yă zauna lafiya kusa da shi, gama yana tsare shi dukan yini, wanda kuma Ubangiji yake ƙauna yana zama a tsakanin kafaɗunsa.”
To Benjamin he said: “May the one the Lord loves be kept safe and secure in the Lord. The Lord always protects him, letting him rest on his shoulders.”
13 Game da Yusuf ya ce, “Bari Ubangiji yă albarkaci ƙasarsa da raɓa mai daraja daga sama a bisa da kuma zurfin ruwan da suke kwance a ƙarƙashi;
To Joseph he said: “May the Lord bless his land with the best gifts of heaven—with the dew and water from the depths below;
14 da abubuwa masu kyau da rana take kawo, da kuma abubuwa mafi kyau da wata zai iya haifar;
with the best crops ripened by the sun and the best produce of the seasons;
15 da zaɓaɓɓun kyautai na daɗaɗɗun duwatsu, da kyawawan amfani na madawwaman tuddai.
with the finest contributions of the ancient mountains and the best materials of the everlasting hills;
16 Tare da kyautai mafi kyau na duniya da cikarta, da tagomashi na wanda yake zama a ƙaramin itace mai ƙonewa. Bari duk waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin sarki a cikin’yan’uwansa.
with the best gifts of the land and everything in it, along with the appreciation of the one who was in the burning bush. May these blessings rest on the head of Joseph like a crown for this prince among his brothers.
17 Cikin daraja yana yi kamar ɗan fari na bijimi; ƙahoninsa ƙahonin ɓauna ne. Tare da su zai tukwiyi al’ummai, har ma da waɗanda suke ƙarshen duniya. Haka dubu dubban Efraim suke; haka dubban Manasse suke.”
He is as majestic as a firstborn bull; his horns are like those of a wild ox. He will use them to gore the nations, driving them to the ends of the earth. The horns represent the ten thousands of Ephraim, and the thousands of Manasseh.”
18 Game da Zebulun ya ce, “Ka yi farin ciki, Zebulun, a fitowarka, kai kuma Issakar, a cikin tentunanka.
To Zebulun he said: “Celebrate, Zebulun, in your travels and Issachar, in your tents.
19 Za su kira mutane zuwa dutse, a can za su miƙa hadayun adalci; za su yi biki a yalwan tekuna, a dukiyoyin da aka ɓoye a cikin yashi.”
They will summon the peoples to a mountain; will offer the appropriate sacrifices there. They will enjoy the rich produce of the seas and from trading on the seashores.”
20 Game da Gad ya ce, “Mai albarka ne wanda ya fadada mazaunin Gad! Gad yana zama a can kamar zaki, yana yayyage a hannu da kai.
To Gad he said: “Blessed is he who makes Gad's territory larger! Gad is like a lion lying in wait, ready to rip off an arm or a head.
21 Ya zaɓi ƙasa mafi kyau wa kansa; aka ajiye masa rabon shugaba. Sa’ad da shugabannin mutane suka taru, ya aikata adalcin Ubangiji da kuma hukuncinsa game da Isra’ila.”
He chose the best land for himself, for he was allocated a ruler's share. He met with the people's leaders; he did what the Lord said was right, following the Lord's regulations for Israel.”
22 Game da Dan ya ce, “Dan ɗan zaki ne, yana tsalle daga Bashan.”
To Dan he said: “Dan is a young lion that leaps out of Bashan.”
23 Game da Naftali ya ce, “Naftali ƙosasshe ne da tagomashin Ubangiji, ya kuma cika albarkarsa; zai gāji gefen kudu zuwa tafki.”
To Naphtali he said: “Naphtali is really favored, full of the Lord's blessing. He shall take over the land to the west and south.”
24 Game da Asher ya ce, “Mafi albarka na’ya’yan, shi ne Asher; bari yă sami tagomashi daga’yan’uwansa, bari kuma yă wanke ƙafafunsa a cikin mai.
To Asher he said: “May Asher be blessed more than all the other sons; may he be favored above his brothers and bathe his feet in olive oil.
25 Madogaran ƙofofinka za su zama ƙarfe da tagulla, ƙarfinka kuma zai zama daidai da kwanakinka.
May the bolts of your gate be strong as iron and bronze, and may you be strong all your life.”
26 “Babu wani kamar Allah na Yeshurun, wanda yake hawa a bisa sammai don yă taimake ka a kan gizagizai kuma a cikin darajarsa.
There is no one like the God of Israel, who rides across the heavens to come to help you; who rides the clouds in majesty.
27 Allah madawwami shi ne mafakarka, a ƙarƙashina kuma madawwamin hannuwa ne. Zai kore abokin gābanka a gabanka, yana cewa, ‘Ka hallaka shi!’
The eternal God is your home, and he holds you up with his everlasting arms. He drives out the enemy ahead of you, and gives the order, “Destroy him!”
28 Haka Isra’ila zai zauna lafiya shi kaɗai; zuriyar Yaƙub a tsare a ƙasar hatsi da sabon ruwan inabi, inda sammai za su zuba raɓa.
As a result Israel lives in peace; Jacob has no trouble in a country of grain and new wine, where the heavens drip with dew.
29 Kai mai albarka ne, ya Isra’ila! Wane ne yake kamar ka, mutanen da Ubangiji ya ceta? Shi ne mafakarka da mai taimakonka da kuma takobinka mai ɗaukaka. Abokan gābanka za su zo neman jinƙai a gabanka, za ka kuwa tattake masujadansu.”
How blessed you are, Israel! Is there anyone like you, a people saved by the Lord? He is the shield that protects you, the sword that gives you confidence. Your enemies will tremble before you, and you shall tread them underfoot.