< Maimaitawar Shari’a 33 >
1 Wannan ita ce albarkar da Musa mutumin Allah ya furta a kan Isra’ilawa, kafin yă rasu.
And this [is] the blessing with which Moses the man of God blessed the children of Israel before his death.
2 Ya ce, “Ubangiji ya zo daga Sinai ya haskaka a bisansu daga Seyir; ya haskaka daga Dutsen Faran. Ya zo tare da dubban tsarkakansa daga kudu, daga gangara dutsensa.
And he said, The Lord is come from Sina, and has appeared from Seir to us, and has hasted out of the mount of Pharan, with the ten thousands of Cades; on his right hand [were] his angels with him.
3 Tabbatacce kai ne wanda yake ƙaunar mutane; dukan tsarkaka suna a hannunka. A ƙafafunka, duk suka rusuna, daga wurinka kuma suka karɓi umarni,
And he spared his people, and all his sanctified ones [are] under thy hands; and they are under thee; and he received of his words
4 dokar Musa ta ba mu dokoki, mallakar taron Yaƙub.
the law which Moses charged us, an inheritance to the assemblies of Jacob.
5 Shi ne sarki a bisa Yeshurun sa’ad da shugabannin mutane suka taru, tare da kabilan Isra’ila.
And he shall be prince with the beloved one, when the princes of the people are gathered together with the tribes of Israel.
6 “Bari Ruben yă rayu, kada yă mutu, kada mutanensa su zama kaɗan.”
Let Ruben live, and not die; and let him be many in number.
7 Ya kuma faɗa wannan game da Yahuda, “Ka ji, ya Ubangiji, kukan Yahuda; ka kawo shi wurin mutanensa. Da hannuwansa ya kāre kansa. Ka taimake shi a kan maƙiyansa!”
And this [is the blessing] of Juda; Hear, Lord, the voice of Juda, and do thou visit his people: his hands shall contend for him, and thou shalt be a help from his enemies.
8 Game da Lawi ya ce, “Tummim da Urim na mutumin da ka nuna masa tagomashi ne. Ka gwada shi a Massa; ka yi faɗa da shi a ruwan Meriba.
And to Levi he said, Give to Levi his manifestations, and his truth to the holy man, whom they tempted in the temptation; they reviled him at the water of strife.
9 Ya yi zancen mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, ‘Ban kula da su ba.’ Bai gane da’yan’uwansa ba, ko yă yarda da’ya’yansa, amma ya kiyaye maganarka ya tsare alkawarinka.
Who says to his father and mother, I have not seen thee; and he knew not his brethren, and he refused to know his sons: he kept thine oracles, and observed thy covenant.
10 Ya koyar da farillanka ga Yaƙub, dokarka kuma ga Isra’ila. Ya miƙa turare a gabanka da kuma hadaya ta ƙonawa ɗungum a kan bagadenka.
They shall declare thine ordinances to Jacob, and thy law to Israel: they shall place incense in [the time of] thy wrath continually upon thine altar.
11 Ka albarkaci ɗaukan dabarunsa, ya Ubangiji, ka kuma ji daɗin aikin hannuwansa. Ka murƙushe kwankwaso waɗanda suka tayar masa; ka bugi abokan gābansa har sai ba su ƙara tashi ba.”
Bless, Lord, his strength, and accept the works of his hands; break the loins of his enemies that have risen up against him, and let not them that hate him rise up.
12 Game da Benyamin ya ce, “Bari ƙaunataccen Ubangiji yă zauna lafiya kusa da shi, gama yana tsare shi dukan yini, wanda kuma Ubangiji yake ƙauna yana zama a tsakanin kafaɗunsa.”
And to Benjamin he said, The beloved of the Lord shall dwell in confidence, and God overshadows him always, and he rested between his shoulders.
13 Game da Yusuf ya ce, “Bari Ubangiji yă albarkaci ƙasarsa da raɓa mai daraja daga sama a bisa da kuma zurfin ruwan da suke kwance a ƙarƙashi;
And to Joseph he said, His land [is] of the blessing of the Lord, of the seasons of sky and dew, and of the deeps of wells below,
14 da abubuwa masu kyau da rana take kawo, da kuma abubuwa mafi kyau da wata zai iya haifar;
and of the fruits of the changes of the sun in season, and of the produce of the months,
15 da zaɓaɓɓun kyautai na daɗaɗɗun duwatsu, da kyawawan amfani na madawwaman tuddai.
from the top of the ancient mountains, and from the top of the everlasting hills,
16 Tare da kyautai mafi kyau na duniya da cikarta, da tagomashi na wanda yake zama a ƙaramin itace mai ƙonewa. Bari duk waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin sarki a cikin’yan’uwansa.
and of the fullness of the land in season: and let the things pleasing to him that dwelt in the bush come on the head of Joseph, and on the crown [of him who was] glorified above his brethren.
17 Cikin daraja yana yi kamar ɗan fari na bijimi; ƙahoninsa ƙahonin ɓauna ne. Tare da su zai tukwiyi al’ummai, har ma da waɗanda suke ƙarshen duniya. Haka dubu dubban Efraim suke; haka dubban Manasse suke.”
His beauty [is as] the firstling of his bull, his horns [are] the horns of a unicorn; with them he shall thrust the nations at once, even from the end of the earth: these [are] the ten thousands of Ephraim, and these [are] the thousands of Manasse.
18 Game da Zebulun ya ce, “Ka yi farin ciki, Zebulun, a fitowarka, kai kuma Issakar, a cikin tentunanka.
And to Zabulon he said, Rejoice, Zabulon, in thy going out, and Issachar in his tents.
19 Za su kira mutane zuwa dutse, a can za su miƙa hadayun adalci; za su yi biki a yalwan tekuna, a dukiyoyin da aka ɓoye a cikin yashi.”
They shall utterly destroy the nations, and ye shall call [men] there, and there offer the sacrifice of righteousness; for the wealth of the sea shall suckle thee, and so shall the marts of them that dwell by the sea-coast.
20 Game da Gad ya ce, “Mai albarka ne wanda ya fadada mazaunin Gad! Gad yana zama a can kamar zaki, yana yayyage a hannu da kai.
And to Gad he said, Blessed [be] he that enlarges Gad: as a lion he rested, having broken the arm and the ruler.
21 Ya zaɓi ƙasa mafi kyau wa kansa; aka ajiye masa rabon shugaba. Sa’ad da shugabannin mutane suka taru, ya aikata adalcin Ubangiji da kuma hukuncinsa game da Isra’ila.”
And he saw his first-fruits, that there the land of the princes gathered with the chiefs of the people was divided; the Lord wrought righteousness, and his judgment with Israel.
22 Game da Dan ya ce, “Dan ɗan zaki ne, yana tsalle daga Bashan.”
And to Dan he said, Dan [is] a lion's whelp, and shall leap out of Basan.
23 Game da Naftali ya ce, “Naftali ƙosasshe ne da tagomashin Ubangiji, ya kuma cika albarkarsa; zai gāji gefen kudu zuwa tafki.”
And to Nephthali he said, Nephthali [has] the fulness of good things; and let him be filled with blessing from the Lord: he shall inherit the west and the south.
24 Game da Asher ya ce, “Mafi albarka na’ya’yan, shi ne Asher; bari yă sami tagomashi daga’yan’uwansa, bari kuma yă wanke ƙafafunsa a cikin mai.
And to Aser he said, Aser [is] blessed with children; and he shall be acceptable to his brethren: he shall dip his foot in oil.
25 Madogaran ƙofofinka za su zama ƙarfe da tagulla, ƙarfinka kuma zai zama daidai da kwanakinka.
His sandal shall be iron and brass; as thy days, so [shall be] thy strength.
26 “Babu wani kamar Allah na Yeshurun, wanda yake hawa a bisa sammai don yă taimake ka a kan gizagizai kuma a cikin darajarsa.
There is not [any such] as the God of the beloved; he who rides upon the heaven [is] thy helper, and the magnificent One of the firmament.
27 Allah madawwami shi ne mafakarka, a ƙarƙashina kuma madawwamin hannuwa ne. Zai kore abokin gābanka a gabanka, yana cewa, ‘Ka hallaka shi!’
And the rule of God shall protect thee, and [that] under the strength of the everlasting arms; and he shall cast forth the enemy from before thy face, saying, Perish.
28 Haka Isra’ila zai zauna lafiya shi kaɗai; zuriyar Yaƙub a tsare a ƙasar hatsi da sabon ruwan inabi, inda sammai za su zuba raɓa.
And Israel shall dwell in confidence alone on the land of Jacob, with corn and wine; and the sky [shall be] misty with dew upon thee.
29 Kai mai albarka ne, ya Isra’ila! Wane ne yake kamar ka, mutanen da Ubangiji ya ceta? Shi ne mafakarka da mai taimakonka da kuma takobinka mai ɗaukaka. Abokan gābanka za su zo neman jinƙai a gabanka, za ka kuwa tattake masujadansu.”
Blessed [art] thou, O Israel; who [is] like to thee, O people saved by the Lord? thy helper shall hold his shield over thee, and [his] sword [is] thy boast; and thine enemies shall speak falsely to thee, and thou shalt tread upon their neck.