< Maimaitawar Shari’a 32 >

1 Ku saurara, ya ku sammai, zan yi magana; bari duniya ta ji maganar bakina.
“Listen to me, [all you who are in the] heavens, and [all you who are on the] earth, listen to what I say [MTY].
2 Bari koyarwata tă zubo kamar ruwan sama kalmomina kuma su sauko kamar raɓa, kamar yayyafi a kan sabuwar ciyawa, kamar ruwan sama mai yawa a kan tsirai marasa ƙarfi.
I wish/desire that my teaching will fall on you like rain drops or be like dew on the ground, and be like a gentle rain on the young plants, like showers on the grass.
3 Zan yi shelar sunan Ubangiji. Ku yabi girman Allahnmu!
I will praise Yahweh [MTY]. And [all you people should] tell others that our God is very great.
4 Shi Dutse ne, ayyukansa cikakku ne, dukan hanyoyinsa kuwa masu adalci ne. Allah mai aminci, wanda ba ya yin rashi gaskiya, shi mai adalci ne, nagari ne kuma.
He is like a rock [MET] [under which we are protected]; [everything] that he does is perfect and completely just/fair [DOU]. He always does what he says that he will do; he never does anything that is wrong.
5 Sun aikata mugunta a gabansa; saboda abin kunyarsu, su ba’ya’yansa ba ne, amma wata muguwar tsara ce, karkatacciya.
“But [you Israeli people] have been very unfaithful to him; because of your sins, you no longer [deserve to] be his children. You are extremely wicked and deceitful [DOU].
6 Haka za ku biya Ubangiji, Ya ku wawaye da kuma mutane marasa hikima? Shi ba Ubanku ba ne, Mahaliccinku, wanda ya yi ku, ya kuma siffanta ku?
You foolish and senseless [DOU] people, (is this the way that you should repay Yahweh [for all that he has done for you]?/this is certainly not the way that you should repay Yahweh [for all that he has done for you].) [RHQ] He is your father; he created you [RHQ]; he caused you to become a nation.
7 Ku tuna da kwanakin dā, ku tuna da tsararrakin da suka wuce tun tuni, Ku tambayi iyayenku, za su faɗa muku, dattawanku, za su kuma bayyana muku.
“Think about [what happened] long ago; consider what happened to your ancestors. Ask your parents, and they will inform you; ask the older people, and they will tell you.
8 Sa’ad da Mafi Ɗaukaka ya ba da al’ummai gādonsu, sa’ad da ya raba dukan’yan adam, ya kafa iyakoki wa mutane bisa ga yawan’ya’yan Isra’ila maza.
When God, who is greater than any other god, long ago divided the people into groups, he assigned to the nations their land. He determined where each people-group should live and (assigned to/chose for) each people-group a god/angel.
9 Gama rabon Ubangiji shi ne mutanensa, Yaƙub shi ne rabon gādonsa.
But Yahweh decided that we would be his people; he chose [us, the descendants of] Jacob, to belong to him.
10 A cikin hamada ya same shi, a jeji marar amfani, inda namomi suke kuka. Ya tsare shi, ya kuma lura da shi; ya bi da shi kamar ƙwayar idonsa,
“He saw [our ancestors] when they were in a desert, wandering in a land (that was desolate/where no people lived). He protected them and took care of them, as every person takes good care of his own eyes. [SIM, IDM]
11 kamar gaggafar da take yawo a kan sheƙarta tana rufe’ya’yanta, ta buɗe fikafikanta don tă kwashe su tă ɗauke su a kafaɗunta.
[Yahweh protected his people] just like an eagle encourages its babies [to fly] and flutters over them [MET], spreading its wings and catching them [if they start to fall].
12 Ubangiji kaɗai ya jagorance shi; babu wani baƙon gunkin da yake tare da shi.
Yahweh was the only one who led them; no other foreign god helped him.
13 Ya sa shi ya hau ƙwanƙolin dutse ya ciyar da shi da amfanin gona. Ya shayar da shi da zuma daga dutse, da kuma mai daga dutsen ƙanƙara,
“[After they entered the land that Yahweh promised to give to them], Yahweh enabled them to rule the hilly areas; they ate the crops that grew in the fields. They found honey in the rocks, and their olive trees [MTY] grew [even] in stony ground.
14 da kindirmo da madara daga shanu da tumaki da ƙibabbun tumaki da awaki, da zaɓaɓɓun ragunan Bashan da kuma ƙwayoyin alkama mafi kyau. Ka sha ruwan inabi ja wur mai kumfa.
The cows gave them plenty of curds/yogurt, the goats gave them plenty of milk, they had well-fed sheep and cattle, they had very good wheat, and they made delicious wine from their grapes.
15 Yeshurun ya yi ƙiba, ya yi kauri; cike da abinci, ya zama da nauyi, ya kuma zama sumul. Ya yashe Allahn da ya yi shi, ya ƙi Dutse Cetonsa.
“The Israeli people became rich and prosperous, but then they rebelled against God; they abandoned him, the one who created them, the one who powerfully saves them.
16 Suka sa shi kishi saboda baƙin allolinsu, suka husata shi da gumakan banƙyamarsu.
So he abandoned them because they started to worship other/strange gods. Because of their worshiping disgusting idols, he became angry.
17 Suka yi hadaya ga aljanu, waɗanda ba Allah ba, ga allolin da ba su sani ba, ga allolin da aka shigo da su daga baya, allolin da kakanninku ba su ji tsoronsu ba.
They offered sacrifices to gods who were [really] demons, gods that their ancestors had never known; they offered sacrifices to gods that they had recently found out about, gods whom your ancestors had never revered.
18 Kuka rabu da Dutsen da ya zama mahaifi gare ku; kuka manta da Allahn da ya haife ku.
They forgot [the true] God, the one who protects them [MET], the one who created them and caused them to live.
19 Ubangiji ya ga wannan ya kuma ƙi su, domin’ya’yansa maza da mata sun husata shi.
“When Yahweh saw that [they had abandoned him], he became angry, so he rejected [the Israeli people, who are like] his sons and daughters.
20 Ya ce, “Zan ɓoye fuskata daga gare su, in ga ƙarshensu; gama su muguwar tsara ce,’ya’ya ne marasa aminci.
He said, ‘They are very wicked/stubborn people, very unfaithful; so I will no longer help them, and then I will watch and see what happens to them.
21 Sun sa ni kishi ta wurin abin da ba allah ba, suka kuma husata ni da gumakansu na wofi. Zan sa su yi kishi ta wurin waɗanda ba mutane ba; zan sa su yi fushi ta wurin al’ummar da ba ta da sani.
They made me very angry because of their worshiping idols, which are not really gods; they have caused me to be [jealous [MET] because I want them to worship only me]. So now, in order to cause them to become jealous, I will send [to attack them an army of] a nation of worthless and foolish people.
22 Gama fushina ya kama wuta, tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za tă cinye duniya da girbinta, tă kuma sa wuta a tussan duwatsu. (Sheol h7585)
I will be very angry, and I will destroy them like a fire that will burn on the earth and all the way down to the place where dead people are [MET]; that fire will destroy the earth and everything that grows on it, and it will even burn what is down under the mountains. (Sheol h7585)
23 “Zan tula masifu a kansu in kuma gama kibiyoyina a kansu.
I will cause them to experience many disasters; [they will feel as though] [MET] I am shooting all my arrows at them.
24 Zan aika da yunwa mai tsanani a kansu, zazzaɓi mai zafi da muguwar annoba; zan aika da haƙoran namun jeji a kansu, da dafin mesa masu ja da ciki.
They will die because of being hungry and because of having hot fevers and because of terrible diseases; I will send wild animals to attack [MTY] them, and poisonous snakes to bite [MTY] them.
25 Waɗanda suke a waje, takobi zai kashe su, a cikin gidajensu kuma tsoro zai mamaye su.’Yan maza da’yan mata za su hallaka, haka ma jarirai da maza masu furfura.
Outside [their houses, their enemies] will kill them [MTY] with swords, and in their homes, [their enemies will cause] them to be terrified. Their enemies will kill young men and young women, and they will kill infants and old people with gray hair.
26 Na ce zan watsar da su in sa a manta da su a tunanin’yan adam.
I wanted to scatter the Israeli people to distant countries in order that no one would ever remember them.
27 Amma ina tsoron tsokanar abokin gāba, don kada abokan gāba su kāsa ganewa har su ce, ‘Hannunmu ne ya yi nasara; ba Ubangiji ne ya aikata dukan wannan ba.’”
But [if I did that], their enemies would wrongly boast that they were the ones who had [gotten rid of my people]; they would say, “We [SYN] are the ones who defeated them; it was not Yahweh who has done all these things.”’
28 Al’ummai ne marasa azanci, babu ganewa a cikinsu.
You Israelis are a nation of people who do not have any sense. None of you is wise.
29 A ce su masu hikima ne har su gane wannan su gane abin da ƙarshensu zai zama!
If you were wise, you would understand [why you would be punished]; you would have realized what was going to happen to you.
30 Yaya mutum guda zai kore dubu, mutum biyu su sa dubu goma su gudu, sai ko Dutsensu ya sayar da su, sai ko Ubangiji ya bashe su.
[You would have realized] why 1,000 [of your soldiers] would be defeated by only one [of the enemy soldiers], and why two of your enemies would chase away 10,000 [Israeli soldiers]. [You would realize that this would happen] only if God, the one who always defended you [MET], had allowed your enemies to defeat you, because he had abandoned you.
31 Gama dutsensu ba kamar Dutsenmu ba ne, abokan gābanmu sun san da haka.
Your enemies know that their gods are not powerful like Yahweh, our God, [so their gods could not have defeated us Israelis].
32 Kuringarsu ta fito daga kuringar Sodom ne, daga gonakin Gomorra kuma.’Ya’yan inabinsu dafi ne, nonnansu masu ɗaci ne.
Your enemies are like [MET] grapevines planted near [the ruins of] Sodom and Gomorrah [cities]; the grapes from those vines are bitter and poisonous;
33 Ruwan inabinsu dafin macizai ne, mugun dafin gamshaƙa ne.
the wine [from those grapes] is like the poison of snakes [DOU].
34 “Ban jibge wannan a ma’ajiya na kuma yimƙe shi a taskokina ba?
[“Yahweh says], ‘I know [RHQ] [what I have planned to do to the Israeli people and to their enemies], and those plans are so secure [that it as though he locked them up] [MET].
35 Sakayya nawa ne, zan kuwa ɗau fansa. A cikin lokaci, ƙafarsu za tă yi santsi; ranar masifarsu ta yi kusa hallakarsu kuma tana gaggautawa a kansu.”
I am the one who will get revenge and pay those enemies back for what they have done [to my people], at the right time for them to be punished [IDM]; they will soon experience disasters, and I will punish/destroy them quickly.’
36 Ubangiji zai shari’anta mutanensa yă kuma ji tausayin bayinsa sa’ad da ya ga ƙarfinsu ya ƙare babu kowa kuma da ya rage, bawa ko’yantacce.
“But Yahweh will see that you who are truly his people, who (are innocent/have not done things that are wrong), and he will be merciful to you. And he will see that you are helpless, and that there are very few of you, slaves or free people, who are still alive.
37 Zai ce, “To, ina allolinsu, dutsen da suka yi mafaka a ciki,
Then Yahweh will ask his people, ‘Where are the gods that you thought would protect you [MET]?
38 allolin da suka ci kitsen hadayunsu suka kuma sha ruwan inabin hadayunsu? Ku sa su tashi su taimake ku mana! Bari su ba ku mafaka!
You gave to those gods the best parts of the animals that you sacrificed, and you poured out wine for them to drink. So, they should begin to help you; they should be the ones who will protect you!
39 “Ku duba yanzu cewa ni ne Shi! Ba wani allah in ban da ni. Nakan kashe in kuma rayar, nakan sa rauni in kuma warkar, ba wanda yake da iko yă cece wani daga hannuna.
“But now you will realize that I, only I, am God; there is no other god who is [a real] god. I am the one who can kill people and who can cause people to live; I can wound people, and I can heal people, and there is no one who can prevent me from doing those things.
40 Na ɗaga hannu sama na kuma furta. Muddin ina raye har abada,
I raise my hand toward heaven and solemnly declare that just as sure as I live forever,
41 sa’ad da na wasa takobi mai walƙiya hannuna kuwa ya cafke shi don yin hukunci, zan ɗau fansa a kan abokan gābana in sāka wa waɗanda suke ƙina.
that when I sharpen my sword, as I [SYN] prepare to punish people, I will get revenge on my enemies; I will pay back those who hate me.
42 Zan sa kibiyoyina su bugu da jini, yayinda takobina yana cin nama, jinin kisassu da na kamammu, kawunan shugabannin abokan gāba.”
I will kill all [of my enemies] with a sword; it will be as though I had arrows that will be covered with their blood. I will kill [MTY] all those whom I capture and cut off their leaders’ heads.’
43 Ku yi farin ciki, ya ku al’ummai, tare da mutanensa, gama zai rama ɗau fansar jinin bayinsa; zai ɗau fansa a kan abokan gābansa yă kuma yi kafara domin ƙasarsa da mutanensa.
“You people of all nations, you as well as his people should praise Yahweh, because Yahweh gets revenge on those who kill the people who serve him; and he cleanses his people’s land which has become defiled because of their sins.”
44 Sai Musa ya zo da Yoshuwa ɗan Nun suka faɗa dukan waɗannan kalmomi wannan waƙa a kunnen mutane.
Joshua and Moses/I recited the words of that song while the Israeli people were listening.
45 Sa’ad da Musa ya gama karanta waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila,
When they/we finished reciting to the Israeli people the words of this song,
46 ya ce musu, “Ku riƙe dukan kalmomin da na furta muku a yau, don ku umarce’ya’yanku su lura, su yi biyayya da dukan kalmomin wannan doka.
Moses/I said, “Never forget all these commands that I have been giving you today. Teach these laws to your children, in order that they will faithfully obey all of them.
47 Ba kalmomi kurum ba ne dominku, amma har ranku ma. Ta wurinsu za ku yi tsawon rai a ƙasar da kuke haye Urdun ku ci gādonta.”
These instructions are very important [LIT]. If [you obey] them, you will live a long time in the land that you are about to cross the Jordan [River] to occupy.”
48 A wannan rana Ubangiji ya ce wa Musa,
On that same day, Yahweh said to Moses/me,
49 “Ka hau Duwatsun Abarim zuwa Dutsen Nebo a Mowab, tsallake daga Yeriko, ka hangi Kan’ana, ƙasar da nake ba wa Isra’ilawa gādo.
“Go to the Abarim Mountain range [here] in the Moab region, across from Jericho. Climb Nebo Mountain, and look [toward the west] to see Canaan land, the land that I am about to give to the Israeli people.
50 A can kan dutsen da ka hau za ka mutu a kuma tara ka ga mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya mutu a Dutsen Hor aka kuma tara shi ga mutanensa.
You will die on that mountain [EUP, DOU], like your [older] brother Aaron died on Hor Mountain.
51 Wannan kuwa domin ku biyu kun fid da aminci gare ni a gaban Isra’ilawa a ruwan Meriba ta Kadesh, a Hamadar Zin kuma saboda ba ku riƙe tsarkina a cikin Isra’ilawa ba.
You will die because both of you disobeyed me in the presence of the Israeli people, when you all were at Meribah Springs near Kadesh [town] in the Zin Desert. You did not honor and respect me in the presence of the Israeli people in the way that I deserve because I am God.
52 Saboda haka, za ka ga ƙasar daga nesa kawai; ba za ka shiga ƙasar da nake ba wa mutanen Isra’ila ba.”
[When you are on that mountain where I told you to go], you will see in the distance in front of you the land that I am about to give to the Israeli people, but you will not enter it.”

< Maimaitawar Shari’a 32 >