< Maimaitawar Shari’a 32 >
1 Ku saurara, ya ku sammai, zan yi magana; bari duniya ta ji maganar bakina.
Lyt til, I Himle, lad mig tale, Jorden høre mine Ord!
2 Bari koyarwata tă zubo kamar ruwan sama kalmomina kuma su sauko kamar raɓa, kamar yayyafi a kan sabuwar ciyawa, kamar ruwan sama mai yawa a kan tsirai marasa ƙarfi.
Lad dryppe som Regn min Lære, lad flyde som Dug mit Ord, som Regnskyl paa unge Spirer, som Regnens Draaber paa Græs.
3 Zan yi shelar sunan Ubangiji. Ku yabi girman Allahnmu!
Thi HERRENS Navn vil jeg forkynde, Ære skal I give vor Gud!
4 Shi Dutse ne, ayyukansa cikakku ne, dukan hanyoyinsa kuwa masu adalci ne. Allah mai aminci, wanda ba ya yin rashi gaskiya, shi mai adalci ne, nagari ne kuma.
Han er Klippen, fuldkomment hans Værk, thi alle hans Veje er Retfærd! En trofast Gud, uden Svig, retfærdig og sanddru er Han.
5 Sun aikata mugunta a gabansa; saboda abin kunyarsu, su ba’ya’yansa ba ne, amma wata muguwar tsara ce, karkatacciya.
Skændselsmennesker sveg ham, en forvendt og vanartet Slægt.
6 Haka za ku biya Ubangiji, Ya ku wawaye da kuma mutane marasa hikima? Shi ba Ubanku ba ne, Mahaliccinku, wanda ya yi ku, ya kuma siffanta ku?
Er det saadan, I lønner HERREN? Du taabelige, uvise Folk! Er han ej din Fader og Skaber, den, som gjorde og danned dig?
7 Ku tuna da kwanakin dā, ku tuna da tsararrakin da suka wuce tun tuni, Ku tambayi iyayenku, za su faɗa muku, dattawanku, za su kuma bayyana muku.
Kom Fortidens Dage i Hu, agt paa henfarne Slægters Aar; spørg din Fader, han skal berette, dine gamle, de skal fortælle dig!
8 Sa’ad da Mafi Ɗaukaka ya ba da al’ummai gādonsu, sa’ad da ya raba dukan’yan adam, ya kafa iyakoki wa mutane bisa ga yawan’ya’yan Isra’ila maza.
Da den Højeste gav Folkene Eje, satte Skel mellem Menneskenes Børn, bestemte han Folkenes Grænser efter Tallet paa Guds Sønner,
9 Gama rabon Ubangiji shi ne mutanensa, Yaƙub shi ne rabon gādonsa.
men HERRENS Del blev Jakob, Israel hans tilmaalte Lod.
10 A cikin hamada ya same shi, a jeji marar amfani, inda namomi suke kuka. Ya tsare shi, ya kuma lura da shi; ya bi da shi kamar ƙwayar idonsa,
Han fandt det i Ørkenlandet, i Ødemarken, blandt Ørkenens Hyl; han værnede det med vaagent Øje og vogtede det som sin Øjesten.
11 kamar gaggafar da take yawo a kan sheƙarta tana rufe’ya’yanta, ta buɗe fikafikanta don tă kwashe su tă ɗauke su a kafaɗunta.
Som Ørnen, der purrer sin Yngel ud og svæver over sine Unger, løftede han det paa sit Vingefang og bar det paa sine Vinger.
12 Ubangiji kaɗai ya jagorance shi; babu wani baƙon gunkin da yake tare da shi.
HERREN var dets eneste Fører, ingen fremmed Gud var hos ham.
13 Ya sa shi ya hau ƙwanƙolin dutse ya ciyar da shi da amfanin gona. Ya shayar da shi da zuma daga dutse, da kuma mai daga dutsen ƙanƙara,
Han lod det færdes over Landets Høje, nærede det med Markens Frugter, lod det suge Honning af Klippen og Olie af Bjergets Flint,
14 da kindirmo da madara daga shanu da tumaki da ƙibabbun tumaki da awaki, da zaɓaɓɓun ragunan Bashan da kuma ƙwayoyin alkama mafi kyau. Ka sha ruwan inabi ja wur mai kumfa.
Surmælk fra Køer, Mælk fra Smaakvæg, dertil Fedt af Lam og Vædre, af Tyre fra Basan og Bukke og Hvedens Fedme tillige, og Drueblod drak du, Vin.
15 Yeshurun ya yi ƙiba, ya yi kauri; cike da abinci, ya zama da nauyi, ya kuma zama sumul. Ya yashe Allahn da ya yi shi, ya ƙi Dutse Cetonsa.
Men da Jesjurun blev fed, slog han bagud, du blev fed, du blev tyk, du blev mæsket; da forskød han Gud, sin Skaber, lod haant om sin Frelses Klippe.
16 Suka sa shi kishi saboda baƙin allolinsu, suka husata shi da gumakan banƙyamarsu.
De æggede ham med fremmede, med Vederstyggeligheder tirrede de ham;
17 Suka yi hadaya ga aljanu, waɗanda ba Allah ba, ga allolin da ba su sani ba, ga allolin da aka shigo da su daga baya, allolin da kakanninku ba su ji tsoronsu ba.
de ofred til Dæmoner, der ej er Guder, til Guder, de ej før kendte til; til nye, der nys var kommet frem, og som ej eders Fædre frygtede.
18 Kuka rabu da Dutsen da ya zama mahaifi gare ku; kuka manta da Allahn da ya haife ku.
Klippen, der avled dig, slog du af Tanke og glemte den Gud, der fødte dig!
19 Ubangiji ya ga wannan ya kuma ƙi su, domin’ya’yansa maza da mata sun husata shi.
Da HERREN saa det, forstødte han dem af Græmmelse over sine Børn
20 Ya ce, “Zan ɓoye fuskata daga gare su, in ga ƙarshensu; gama su muguwar tsara ce,’ya’ya ne marasa aminci.
og sagde: »Jeg vil skjule mit Aasyn for dem og se, hvad Ende det tager med dem; thi de er en bundfalsk Slægt, Børn, som er uden Troskab;
21 Sun sa ni kishi ta wurin abin da ba allah ba, suka kuma husata ni da gumakansu na wofi. Zan sa su yi kishi ta wurin waɗanda ba mutane ba; zan sa su yi fushi ta wurin al’ummar da ba ta da sani.
de ægged mig med det, der ikke er Gud, tirrede mig ved deres tomme Gøgl: Jeg vil ægge dem med det, der ikke er et Folk, tirre dem ved et Folk af Daarer.
22 Gama fushina ya kama wuta, tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za tă cinye duniya da girbinta, tă kuma sa wuta a tussan duwatsu. (Sheol )
Thi der flammer en Ild i min Vrede, som brænder til Dødsrigets Dyb; den fortærer Jorden med dens Grøde og antænder Bjergenes Grunde. (Sheol )
23 “Zan tula masifu a kansu in kuma gama kibiyoyina a kansu.
Jeg hober Ulykker over dem og opbruger mine Pile imod dem.
24 Zan aika da yunwa mai tsanani a kansu, zazzaɓi mai zafi da muguwar annoba; zan aika da haƙoran namun jeji a kansu, da dafin mesa masu ja da ciki.
De udmagres af Sult og hentæres af Pestglød og giftig Sot; saa sender jeg Vilddyrs Tænder og Slangers Gift imod dem.
25 Waɗanda suke a waje, takobi zai kashe su, a cikin gidajensu kuma tsoro zai mamaye su.’Yan maza da’yan mata za su hallaka, haka ma jarirai da maza masu furfura.
Ude slaar Sværdet Børnene ned og inde i Kamrene Rædselen baade Yngling og Jomfru, diende Børn og graanende Mænd.
26 Na ce zan watsar da su in sa a manta da su a tunanin’yan adam.
Jeg satte mig for at blæse dem bort og slette deres Minde blandt Mennesker ud,
27 Amma ina tsoron tsokanar abokin gāba, don kada abokan gāba su kāsa ganewa har su ce, ‘Hannunmu ne ya yi nasara; ba Ubangiji ne ya aikata dukan wannan ba.’”
men jeg frygtede, at Fjenden skulde volde mig Græmmelse, deres Avindsmænd tage fejl og tænke: Det var vor egen Haand, der var stærk, ej HERREN, der gjorde alt dette.
28 Al’ummai ne marasa azanci, babu ganewa a cikinsu.
Thi de er et raadvildt Folk, og i dem er der ikke Forstand.
29 A ce su masu hikima ne har su gane wannan su gane abin da ƙarshensu zai zama!
Var de vise, forstod de det og indsaa, hvad der venter dem selv!
30 Yaya mutum guda zai kore dubu, mutum biyu su sa dubu goma su gudu, sai ko Dutsensu ya sayar da su, sai ko Ubangiji ya bashe su.
Hvor skulde een kunne forfølge tusind, og to slaa ti Tusind paa Flugt, hvis ikke deres Klippe havde solgt dem og HERREN givet dem til Pris!
31 Gama dutsensu ba kamar Dutsenmu ba ne, abokan gābanmu sun san da haka.
Thi deres Klippe er ikke som vor, det ved vore Fjender bedst selv!
32 Kuringarsu ta fito daga kuringar Sodom ne, daga gonakin Gomorra kuma.’Ya’yan inabinsu dafi ne, nonnansu masu ɗaci ne.
Thi fra Sodoma stammer deres Vinstok og fra Gomorras Marker; deres Druer er giftige Druer, og beske er deres Klaser;
33 Ruwan inabinsu dafin macizai ne, mugun dafin gamshaƙa ne.
som Dragegift er deres Vin, som Øglers gruelige Edder.
34 “Ban jibge wannan a ma’ajiya na kuma yimƙe shi a taskokina ba?
Er ej dette forvaret hos mig, forseglet i mine Gemmer
35 Sakayya nawa ne, zan kuwa ɗau fansa. A cikin lokaci, ƙafarsu za tă yi santsi; ranar masifarsu ta yi kusa hallakarsu kuma tana gaggautawa a kansu.”
til Hævnens og Regnskabets Dag, den Stund, deres Fod skal vakle? Thi deres Undergangs Dag stunder til; hvad der venter dem, kommer i Hast.«
36 Ubangiji zai shari’anta mutanensa yă kuma ji tausayin bayinsa sa’ad da ya ga ƙarfinsu ya ƙare babu kowa kuma da ya rage, bawa ko’yantacce.
Thi Ret skaffer HERREN sit Folk og forbarmer sig over sine Tjenere, thi han ser, deres Kraft er brudt, det er ude med hver og en.
37 Zai ce, “To, ina allolinsu, dutsen da suka yi mafaka a ciki,
Da spørger han: »Hvor er nu deres Gud, Klippen, paa hvem de forlod sig,
38 allolin da suka ci kitsen hadayunsu suka kuma sha ruwan inabin hadayunsu? Ku sa su tashi su taimake ku mana! Bari su ba ku mafaka!
som aad deres Slagtofres Fedme og drak deres Drikofres Vin? Lad dem rejse sig og hjælpe eder, lad dem være eder et Skjul!
39 “Ku duba yanzu cewa ni ne Shi! Ba wani allah in ban da ni. Nakan kashe in kuma rayar, nakan sa rauni in kuma warkar, ba wanda yake da iko yă cece wani daga hannuna.
Erkend nu, at jeg, jeg er Gud uden anden Gud ved min Side. Jeg døder, jeg gør levende, jeg saarer, og jeg læger, og ingen kan frelse fra min Haand.
40 Na ɗaga hannu sama na kuma furta. Muddin ina raye har abada,
Thi jeg løfter min Haand mod Himlen og siger: Saa sandt jeg lever evindelig,
41 sa’ad da na wasa takobi mai walƙiya hannuna kuwa ya cafke shi don yin hukunci, zan ɗau fansa a kan abokan gābana in sāka wa waɗanda suke ƙina.
jeg hvæsser mit lynende Sværd, og min Haand tager fat paa Dommen, jeg hævner mig paa mine Fjender, øver Gengæld mod mine Avindsmænd.
42 Zan sa kibiyoyina su bugu da jini, yayinda takobina yana cin nama, jinin kisassu da na kamammu, kawunan shugabannin abokan gāba.”
Mine Pile gør jeg drukne af Blod, og mit Sværd skal svælge i Kød, i faldnes og fangnes Blod og fjendtlige Høvdingers Hoveder!«
43 Ku yi farin ciki, ya ku al’ummai, tare da mutanensa, gama zai rama ɗau fansar jinin bayinsa; zai ɗau fansa a kan abokan gābansa yă kuma yi kafara domin ƙasarsa da mutanensa.
I Folkeslag, pris hans Folk, thi han hævner sine Tjeneres Blod; han hævner sig paa sine Fjender, og skaffer sit Folks Land Soning!
44 Sai Musa ya zo da Yoshuwa ɗan Nun suka faɗa dukan waɗannan kalmomi wannan waƙa a kunnen mutane.
Og Moses kom og fremsagde hele denne Sang for Folket, han og Josua, Nuns Søn.
45 Sa’ad da Musa ya gama karanta waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila,
Og da Moses var færdig med at fremsige alle disse Ord for hele Israel,
46 ya ce musu, “Ku riƙe dukan kalmomin da na furta muku a yau, don ku umarce’ya’yanku su lura, su yi biyayya da dukan kalmomin wannan doka.
sagde han til dem: »Læg eder alle de Ord paa Sinde, som jeg i Dag har vidnet imod eder, for at du kan paalægge dine Sønner dem, at de omhyggeligt maa handle efter alle denne Lovs Bud;
47 Ba kalmomi kurum ba ne dominku, amma har ranku ma. Ta wurinsu za ku yi tsawon rai a ƙasar da kuke haye Urdun ku ci gādonta.”
thi det er ikke tomme Ord uden Betydning for eder, men af dem afhænger eders Liv, og ved at følge det Ord skal I faa et langt Liv i det Land, som I skal ind og tage i Besiddelse efter at være gaaet over Jordan.«
48 A wannan rana Ubangiji ya ce wa Musa,
Selv samme Dag talede HERREN til Moses og sagde:
49 “Ka hau Duwatsun Abarim zuwa Dutsen Nebo a Mowab, tsallake daga Yeriko, ka hangi Kan’ana, ƙasar da nake ba wa Isra’ilawa gādo.
»Stig op paa Abarimbjerget der, Nebobjerget i Moabs Land over for Jeriko, og se ud over Kana'ans Land, som jeg vil give Israeliterne i Eje!
50 A can kan dutsen da ka hau za ka mutu a kuma tara ka ga mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya mutu a Dutsen Hor aka kuma tara shi ga mutanensa.
Og saa skal du dø paa det Bjerg, du bestiger, og samles til din Slægt, ligesom din Broder Aron døde paa Bjerget Hor og samledes til sin Slægt,
51 Wannan kuwa domin ku biyu kun fid da aminci gare ni a gaban Isra’ilawa a ruwan Meriba ta Kadesh, a Hamadar Zin kuma saboda ba ku riƙe tsarkina a cikin Isra’ilawa ba.
fordi I handlede troløst imod mig iblandt Israeliterne ved Meribat-Kadesj's Vand i Zins Ørken, fordi I ikke helligede mig iblandt Israeliterne.
52 Saboda haka, za ka ga ƙasar daga nesa kawai; ba za ka shiga ƙasar da nake ba wa mutanen Isra’ila ba.”
Thi her ovre fra skal du se ud over Landet, men du skal ikke komme derind, ind i det Land, jeg vil give Israeliterne!«