< Maimaitawar Shari’a 31 >
1 Sai Musa ya fita ya kuma faɗa waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila cewa,
UMozisi wasehamba wakhuluma lamazwi kuIsrayeli wonke,
2 “Yanzu shekaruna ɗari da ashirin ne, ba na iya kaiwa da komowa. Ubangiji ya ce mini, ‘Ba za ka haye Urdun ba.’
wathi kubo: Ngileminyaka elikhulu lamatshumi amabili lamuhla; kangiselamandla okuphuma lokungena. LeNkosi yathi kimi: Kawuyikuyichapha le iJordani.
3 Ubangiji Allahnku kansa zai haye a gabanku. Zai hallaka waɗannan al’ummai da suke gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu. Yoshuwa shi ma zai haye a gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
INkosi uNkulunkulu wakho, yona izachapha phambi kwakho, yona izachitha lezizizwe zisuke phambi kwakho, ukuze udle ilifa lazo. UJoshuwa, yena uzachapha phambi kwakho, njengokutsho kweNkosi.
4 Ubangiji zai yi da su, yadda ya yi da Sihon da Og, sarakunan Amoriyawa, waɗanda ya hallaka tare da ƙasarsu.
LeNkosi izakwenza kuzo njengokwenza kwayo kuSihoni lakuOgi, amakhosi amaAmori, lelizweni lawo, ewachithileyo.
5 Ubangiji zai bashe su gare ku, dole kuma ku yi musu dukan abin da na umarce ku.
INkosi izazinikela-ke phambi kwenu, ukuze lenze kuzo njengokwemilayo yonke engililaye yona.
6 Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro, ko ku firgita saboda su, gama Ubangiji Allahnku yana tafe tare da ku, ba zai taɓa barinku ko yă yashe ku ba.”
Qinani, lime isibindi, lingesabi, lingatshaywa luvalo ngenxa yazo; ngoba iNkosi uNkulunkulu wakho, yiyo ehamba lawe; kayiyikukulahla, kayiyikukudela.
7 Sai Musa ya kira Yoshuwa, ya ce masa a gaban dukan Isra’ila, “Ka ƙarfafa, ka kuma yi ƙarfin hali, gama dole ka tafi tare da mutanen nan zuwa cikin ƙasar da Ubangiji ya rantse cewa za ba wa kakanninku, dole kuma ka raba ta gare su ta zama gādonsu.
UMozisi wasembiza uJoshuwa, wathi kuye phambi kwamehlo kaIsrayeli wonke: Qina, ume isibindi; ngoba wena uzangena lalababantu elizweni iNkosi eyalifungela oyise ukubanika lona; uzabenza badle ilifa lalo.
8 Ubangiji kansa yana tafe a gabanka, zai kuma kasance tare da kai, ba zai taɓa barinka ko yă yashe ka ba. Kada ka ji tsoro; kada kuma ka karai.”
Njalo iNkosi, yiyo ehamba phambi kwakho; yona izakuba lawe, ingakulahli, ingakudeli; ungesabi, ungakhathazeki.
9 Sai Musa ya rubuta wannan doka ya kuma ba da ita ga firistoci,’ya’yan Lawi maza, waɗanda sukan ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji, da kuma dukan dattawan Isra’ila.
UMozisi wasewubhala lumlayo, wawunika abapristi, amadodana kaLevi, ababethwala umtshokotsho wesivumelwano seNkosi, lakubo bonke abadala bakoIsrayeli.
10 Sa’an nan Musa ya umarce su ya ce, “A ƙarshen kowace shekara bakwai, a shekara ta yafe basusuwa, a lokacin Bikin Tabanakul,
UMozisi wasebalaya esithi: Ekupheleni kweminyaka eyisikhombisa, ngesikhathi esimisiweyo somnyaka wenkululeko, emkhosini wamadumba,
11 sa’ad da dukan Isra’ila suka zo, don su bayyana a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da zai zaɓa, za ku karanta wannan doka a gabansu, a kunnuwansu.
lapho uIsrayeli wonke esefike ukubonakala phambi kweNkosi uNkulunkulu wakho endaweni ezayikhetha, uwubale lumlayo phambi kukaIsrayeli wonke endlebeni zabo.
12 Ku tattara mutane, maza, mata da kuma yara, da baƙin da suke zama a cikin garuruwanku, saboda su saurara, su kuma koyi tsoron Ubangiji Allahnku, su lura, su bi dukan kalmomin wannan doka.
Buthanisa abantu, abesilisa labesifazana labantwana, lowemzini wakho ophakathi kwamasango akho, ukuze bezwe, lokuze bafunde, bayesabe iNkosi uNkulunkulu wenu, bagcine ukwenza wonke amazwi alumlayo.
13 ’Ya’yansu, waɗanda ba su san wannan doka ba, dole su ji ta, su kuma koyi tsoron Ubangiji Allahnku muddin ranku a ƙasar da kuke haye Urdun ku ci gādonta.”
Labantwana babo abangaziyo bezwe, bafunde ukuyesaba iNkosi uNkulunkulu wenu, zonke izinsuku zokuphila kwenu, elizweni elichapha iJordani lisiya kulo ukudla ilifa lalo.
14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Yanzu ranar mutuwarka ta yi kusa. Ka kira Yoshuwa, ku shigo Tentin Sujada, inda zan ba shi ragamar aiki.” Saboda haka Musa da Yoshuwa suka zo, suka kuma shiga Tentin Sujada.
INkosi yasisithi kuMozisi: Khangela, insuku zakho zokufa sezisondele; biza uJoshuwa, zimiseni ethenteni lenhlangano ukuze ngimlaye. UMozisi loJoshuwa bahamba-ke, bazimisa ethenteni lenhlangano.
15 Ubangiji kuwa ya bayyana a Tentin Sujada a cikin ginshiƙin girgije, sai girgijen ya tsaya a ƙofar Tentin Sujada.
INkosi yasibonakala ethenteni ensikeni yeyezi; lensika yeyezi yema phezu komnyango wethente.
16 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Za ka huta tare da kakanninka, waɗannan mutane kuwa ba da daɗewa ba za su yi karuwanci ga baƙin alloli na ƙasar da za su shiga. Za su yashe ni su kuma karya alkawarin da na yi da su.
INkosi yasisithi kuMozisi: Khangela, uzalala laboyihlo; lalababantu bazasukuma baphinge ngokulandela onkulunkulu bezizweni belizwe, lapho abaya khona phakathi kwabo, bangitshiye, bephule isivumelwano sami engisenze labo.
17 A wannan rana zan yi fushi da su, in kuma yashe su; zan ɓoye fuskata daga gare su, za a kuwa hallaka su. Masifu masu yawa da wahaloli masu yawa za su auka musu, a wannan rana kuwa za su ce, ‘Masifun nan sun same mu domin Allahnmu ba ya tare da mu’
Lentukuthelo yami izabavuthela ngalolosuku, ngibatshiye, ngibafihlele ubuso bami, ukuze babe yikudla, behlelwe ngokubi okunengi lezinhlupheko, baze bathi ngalolosuku: Angithi lobububi busehlele ngoba uNkulunkulu wethu kakho phakathi kwethu?
18 Tabbatacce kuwa, zan ɓoye musu fuskata saboda muguntar da suka aikata, suka kuma bi gumaka.
Lami ngizafihla lokufihla ubuso bami ngalolosuku ngenxa yobubi bonke ababenzileyo, ngoba bephendukele kwabanye onkulunkulu.
19 “To, sai ka rubuta wannan waƙa domin kanka, ka koya wa Isra’ilawa, ka kuma sa su rera ta, don tă zama shaida a kansu.
Ngakho-ke zibhaleleni lingoma, uyifundise abantwana bakoIsrayeli; uyifake emlonyeni wabo ukuze lingoma ibe yibufakazi kimi obumelene labantwana bakoIsrayeli.
20 Sa’ad da na kawo su cikin ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa ga kakanninsu, sa’ad da kuma suka ci suka ƙoshi, suka kuma yi ƙiba, za su juya ga waɗansu alloli su bauta musu, su ƙi ni, su kuma karya alkawarina.
Lapho sengibangenisile elizweni engalifungela oyise, eligeleza uchago loluju, sebedlile basutha, bazimuka, bazaphendukela kwabanye onkulunkulu, babakhonze, bangidelele, bephule isivumelwano sami.
21 Sa’ad da kuma masifu masu yawa da wahaloli masu yawa suka auko musu, wannan waƙa za tă zama shaida a kansu, domin zuriyarsu ba za tă manta da ita ba. Na san abin da za su iya yi, kafin ma in kawo su cikin ƙasar da na yi musu alkawari da rantsuwa.”
Kuzakuthi-ke, nxa sebehlelwe ngokubi okunengi lezinhlupheko, lingoma izaphendula phambi kobuso babo ibe yibufakazi; ngoba kayiyikukhohlakala emlonyeni wenzalo yabo. Ngoba ngiyawazi amacebo abo abawenzayo lamuhla, ngingakabangenisi elizweni engifunge ngalo.
22 Sai Musa ya rubuta wannan waƙa a wannan rana, ya kuma koya wa Isra’ilawa.
UMozisi wasebhala lingoma ngalolosuku, wayifundisa abantwana bakoIsrayeli.
23 Ubangiji ya ba wa Yoshuwa ɗan Nun wannan umarni, “Ka ƙarfafa, ka kuma yi ƙarfin hali, gama za ka kawo Isra’ilawa cikin ƙasar da na yi musu alkawari da rantsuwa, ni kaina kuwa zan kasance tare da kai.”
Yasilaya uJoshuwa indodana kaNuni yathi: Qina, ume isibindi, ngoba wena uzabangenisa abantwana bakoIsrayeli elizweni engabafungela lona; lami ngizakuba lawe.
24 Bayan Musa ya gama rubuta kalmomin dokan nan a littafi daga farko zuwa ƙarshe,
Kwasekusithi uMozisi eseqedile ukubhala amazwi alumlayo egwalweni, aze aphela,
25 sai ya ba wa Lawiyawa, waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji wannan umarni,
uMozisi walaya amaLevi ayethwala umtshokotsho wesivumelwano seNkosi esithi:
26 “Ku ɗauki wannan Littafin Doka ku sa shi kusa da akwatin alkawarin Ubangiji Allahnku. A can zai kasance a matsayin shaida a kanku.
Thathani lolugwalo lomlayo, lilubeke eceleni komtshokotsho wesivumelwano seNkosi uNkulunkulu wenu, ukuze lube khona, kube yibufakazi obumelene lawe.
27 Gama na sani yadda kuke’yan tawaye da masu taurinkai. In kuna yin tawaye ga Ubangiji tun ina da rai tare da ku, yaya tawayen da za ku yi masa bayan na rasu!
Ngoba mina ngiyazi umvukela wakho, lentamo yakho elukhuni; khangelani, ngisaphila lani lamuhla, belingabavukeli beNkosi; pho, kangakanani emva kokufa kwami?
28 Ku tattara dukan dattawan kabilanku, da kuma dukan hafsoshinku a gabana, saboda in faɗa waɗannan kalmomi a kunnuwansu, in kuma kira ga sama da ƙasa su zama shaida a kansu.
Buthanisani kimi bonke abadala bezizwe zenu lenduna zenu ukuze ngikhulume lamazwi endlebeni zabo, ngibize amazulu lomhlaba ukuba ngabafakazi bamelane labo.
29 Gama na san cewa bayan rasuwata, tabbatacce za ku lalace gaba ɗaya, ku juye daga hanyar da na umarce ku. A kwanaki masu zuwa, masifa za tă auka muku saboda za ku aikata mugunta a gaban Ubangiji, ku tsokane shi har yă yi fushi ta wurin abin da hannuwanku suka yi.”
Ngoba ngiyazi ukuthi emva kokufa kwami lizakona lokona, liphambuke endleleni engililaye yona; lizakwehlelwa ngokubi ngensuku ezizayo, ngoba lizakwenza okubi emehlweni eNkosi, liyithukuthelise ngomsebenzi wezandla zenu.
30 Sai Musa ya karanta kalmomin waƙar daga farko zuwa ƙarshe a kunnuwan dukan taron jama’ar Isra’ila.
UMozisi wasekhuluma amazwi alingoma endlebeni zebandla lonke lakoIsrayeli, aze aphela.