< Maimaitawar Shari’a 31 >
1 Sai Musa ya fita ya kuma faɗa waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila cewa,
Mojsije dođe da upravi ove riječi svemu Izraelu:
2 “Yanzu shekaruna ɗari da ashirin ne, ba na iya kaiwa da komowa. Ubangiji ya ce mini, ‘Ba za ka haye Urdun ba.’
“Meni je danas sto dvadeset godina”, - reče im. “Ne mogu više izlaziti i ulaziti. A Jahve mi je rekao: 'Nećeš prijeći ovog Jordana!'
3 Ubangiji Allahnku kansa zai haye a gabanku. Zai hallaka waɗannan al’ummai da suke gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu. Yoshuwa shi ma zai haye a gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
Sam Jahve, Bog tvoj, pred tobom će prijeći; on će pred tobom potući one narode da ih otjerate s posjeda. Jošua će pred tobom ići, kako je Jahve rekao.
4 Ubangiji zai yi da su, yadda ya yi da Sihon da Og, sarakunan Amoriyawa, waɗanda ya hallaka tare da ƙasarsu.
Jahve će postupiti s njima kako je postupio sa Sihonom i Ogom, amorejskim kraljevima, i njihovom zemljom kad ih uništi.
5 Ubangiji zai bashe su gare ku, dole kuma ku yi musu dukan abin da na umarce ku.
Pred vas će ih Jahve položiti, a vi ćete s njima postupati prema svim naredbama koje sam vam dao.
6 Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro, ko ku firgita saboda su, gama Ubangiji Allahnku yana tafe tare da ku, ba zai taɓa barinku ko yă yashe ku ba.”
Ohrabrite se i budite odlučni! Ne bojte se i nemojte prÓedati pred njima. TÓa sam Jahve, Bog tvoj, ide s tobom; neće te zapustiti niti će te ostaviti.”
7 Sai Musa ya kira Yoshuwa, ya ce masa a gaban dukan Isra’ila, “Ka ƙarfafa, ka kuma yi ƙarfin hali, gama dole ka tafi tare da mutanen nan zuwa cikin ƙasar da Ubangiji ya rantse cewa za ba wa kakanninku, dole kuma ka raba ta gare su ta zama gādonsu.
Tada Mojsije zovnu Jošuu pa mu reče pred svim Izraelom: “Ohrabri se i budi odlučan! Jer ti ćeš ići s ovim narodom u zemlju za koju se Jahve zakle ocima njihovim da će im je dati; ti ćeš im je predavati u baštinu.
8 Ubangiji kansa yana tafe a gabanka, zai kuma kasance tare da kai, ba zai taɓa barinka ko yă yashe ka ba. Kada ka ji tsoro; kada kuma ka karai.”
Sam Jahve ide pred tobom; on će s tobom biti; neće te zapustiti niti će te ostaviti. Ne boj se i ne dršći!”
9 Sai Musa ya rubuta wannan doka ya kuma ba da ita ga firistoci,’ya’yan Lawi maza, waɗanda sukan ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji, da kuma dukan dattawan Isra’ila.
Mojsije napisa ovaj Zakon i predade ga svećenicima, sinovima Levijevim, koji su nosili Kovčeg saveza Jahvina, i svim izraelskim starješinama.
10 Sa’an nan Musa ya umarce su ya ce, “A ƙarshen kowace shekara bakwai, a shekara ta yafe basusuwa, a lokacin Bikin Tabanakul,
Mojsije im naredi: “Svake sedme godine - godine oprosne - na Blagdan sjenica,
11 sa’ad da dukan Isra’ila suka zo, don su bayyana a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da zai zaɓa, za ku karanta wannan doka a gabansu, a kunnuwansu.
kad dođe sav Izrael da vidi lice Jahve, Boga tvoga, na mjestu koje on odabere, pročitaj ovaj Zakon u nazočnosti svega Izraela.
12 Ku tattara mutane, maza, mata da kuma yara, da baƙin da suke zama a cikin garuruwanku, saboda su saurara, su kuma koyi tsoron Ubangiji Allahnku, su lura, su bi dukan kalmomin wannan doka.
Saberi narod - ljude, žene, djecu i došljaka što bude u tvojim gradovima - da čuju i da nauče bojati se Jahve, Boga vašega, pa da drže i vrše sve riječi ovog Zakona.
13 ’Ya’yansu, waɗanda ba su san wannan doka ba, dole su ji ta, su kuma koyi tsoron Ubangiji Allahnku muddin ranku a ƙasar da kuke haye Urdun ku ci gādonta.”
Sinovi njihovi, koji to još ne znaju, čut će i naučit će bojati se Jahve, Boga vašega, sve vrijeme dok budete živjeli na zemlji što ćete je, prešavši Jordan, zaposjesti.”
14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Yanzu ranar mutuwarka ta yi kusa. Ka kira Yoshuwa, ku shigo Tentin Sujada, inda zan ba shi ragamar aiki.” Saboda haka Musa da Yoshuwa suka zo, suka kuma shiga Tentin Sujada.
Jahve reče Mojsiju: “Evo se bliži vrijeme tvoje smrti. Zovni Jošuu i nađite se u Šatoru sastanka da mu dam zapovijedi.” Mojsije i Jošua dođu u Šator sastanka.
15 Ubangiji kuwa ya bayyana a Tentin Sujada a cikin ginshiƙin girgije, sai girgijen ya tsaya a ƙofar Tentin Sujada.
U Šatoru pokaže se Jahve u stupu od oblaka. Stup od oblaka stajao je na ulazu u Šator.
16 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Za ka huta tare da kakanninka, waɗannan mutane kuwa ba da daɗewa ba za su yi karuwanci ga baƙin alloli na ƙasar da za su shiga. Za su yashe ni su kuma karya alkawarin da na yi da su.
Jahve reče Mojsiju: “Evo ćeš naskoro počinuti sa svojim ocima. A narod će se ovaj dići da čini blud idući za tuđim bogovima one zemlje u koju će naskoro ući; mene će napustiti i prekršit će moj Savez što ga s njim sklopih.
17 A wannan rana zan yi fushi da su, in kuma yashe su; zan ɓoye fuskata daga gare su, za a kuwa hallaka su. Masifu masu yawa da wahaloli masu yawa za su auka musu, a wannan rana kuwa za su ce, ‘Masifun nan sun same mu domin Allahnmu ba ya tare da mu’
I onda će se izliti moj gnjev na nj. Ostavit ću ih tada i sakriti od njih svoje lice da budu proždirani. Snaći će ih mnoga zla i nevolje i onda će reći: 'Zar me ne snalaze ove nevolje zbog toga što Bog moj nije u mojoj sredini?'
18 Tabbatacce kuwa, zan ɓoye musu fuskata saboda muguntar da suka aikata, suka kuma bi gumaka.
A ja ću sasvim sakriti svoje lice u taj dan, zbog svega zla što ga budu činili okrećući se drugim bogovima.
19 “To, sai ka rubuta wannan waƙa domin kanka, ka koya wa Isra’ilawa, ka kuma sa su rera ta, don tă zama shaida a kansu.
Pišite sada sebi ovu pjesmu. Neka je nauče Izraelci! Stavi je u njihova usta da mi ova pjesma bude svjedokom protiv Izraelaca.
20 Sa’ad da na kawo su cikin ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa ga kakanninsu, sa’ad da kuma suka ci suka ƙoshi, suka kuma yi ƙiba, za su juya ga waɗansu alloli su bauta musu, su ƙi ni, su kuma karya alkawarina.
Kad ih dovedem u zemlju kojom teče med i mlijeko i za koju se zakleh ocima njihovim i kad se najedu, nasite i ugoje, okrenut će se oni drugim bogovima i njima će iskazivati štovanje; mene će prezreti i prekršiti moj Savez.
21 Sa’ad da kuma masifu masu yawa da wahaloli masu yawa suka auko musu, wannan waƙa za tă zama shaida a kansu, domin zuriyarsu ba za tă manta da ita ba. Na san abin da za su iya yi, kafin ma in kawo su cikin ƙasar da na yi musu alkawari da rantsuwa.”
A kad ih snađu mnoge nesreće i nevolje, ova pjesma, jer je njihovo potomstvo neće nikada zaboraviti, pružit će svjedočanstvo protiv njih. Jer znam ja njihove osnove i što već danas snuju, prije nego sam ih i doveo u zemlju koju im pod zakletvom obećah.”
22 Sai Musa ya rubuta wannan waƙa a wannan rana, ya kuma koya wa Isra’ilawa.
Toga dana napisa Mojsije ovu pjesmu i nauči Izraelce pjesmi.
23 Ubangiji ya ba wa Yoshuwa ɗan Nun wannan umarni, “Ka ƙarfafa, ka kuma yi ƙarfin hali, gama za ka kawo Isra’ilawa cikin ƙasar da na yi musu alkawari da rantsuwa, ni kaina kuwa zan kasance tare da kai.”
Nunovu sinu Jošui naloži: “Ohrabri se i budi odlučan! Jer ti ćeš uvesti Izraelce u zemlju za koju sam im se zakleo. I ja ću biti s tobom.”
24 Bayan Musa ya gama rubuta kalmomin dokan nan a littafi daga farko zuwa ƙarshe,
Kad Mojsije napisa riječi ovoga Zakona u knjigu,
25 sai ya ba wa Lawiyawa, waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji wannan umarni,
tada naredi Levijevcima, koji su nosili Kovčeg saveza Jahvina:
26 “Ku ɗauki wannan Littafin Doka ku sa shi kusa da akwatin alkawarin Ubangiji Allahnku. A can zai kasance a matsayin shaida a kanku.
“Uzmite knjigu ovoga Zakona i položite je uz Kovčeg saveza Jahvina. Neka ondje bude svjedokom protiv tebe!
27 Gama na sani yadda kuke’yan tawaye da masu taurinkai. In kuna yin tawaye ga Ubangiji tun ina da rai tare da ku, yaya tawayen da za ku yi masa bayan na rasu!
TÓa znam ja tvoju buntovnost i tvoju tvrdu šiju. Evo i danas, dok još s vama živim, bunite se protiv Jahve. A kako li nećete kad ja umrem!
28 Ku tattara dukan dattawan kabilanku, da kuma dukan hafsoshinku a gabana, saboda in faɗa waɗannan kalmomi a kunnuwansu, in kuma kira ga sama da ƙasa su zama shaida a kansu.
Saberite k meni sve starješine svojih plemena i svoje nadglednike da na njihove uši kažem ove riječi te da protiv njih uzmem za svjedoke nebo i zemlju.
29 Gama na san cewa bayan rasuwata, tabbatacce za ku lalace gaba ɗaya, ku juye daga hanyar da na umarce ku. A kwanaki masu zuwa, masifa za tă auka muku saboda za ku aikata mugunta a gaban Ubangiji, ku tsokane shi har yă yi fushi ta wurin abin da hannuwanku suka yi.”
Jer znam ja da ćete se nakon moje smrti izopačiti i skrenuti s puta koji sam vam odredio; nesreća će vas snaći u budućim vremenima kad budete činili što je Jahvi nemilo i gnjevili ga djelima ruku svojih.”
30 Sai Musa ya karanta kalmomin waƙar daga farko zuwa ƙarshe a kunnuwan dukan taron jama’ar Isra’ila.
A onda, na uši sve zajednice izraelske, Mojsije izgovori do kraja riječi ove pjesme: