< Maimaitawar Shari’a 30 >

1 Sa’ad da dukan albarku da la’anonin nan da na sa a gabanku suka zo muku, kuka kuma sa su a zuciya, a duk inda Ubangiji Allahnku ya watsar da ku a cikin al’ummai,
Or, quand toutes ces choses, que je t'ai représentées, seront venues sur toi, soit la bénédiction, soit la malédiction, et que tu les rappelleras à ton cœur, parmi toutes les nations où l'Éternel ton Dieu t'aura chassé;
2 sa’ad da kuma ku da’ya’yanku kuka komo ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi biyayya da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, bisa ga kome da na umarce ku a yau,
Et que tu te convertiras à l'Éternel ton Dieu, et que tu obéiras à sa voix, de tout ton cœur et de toute ton âme, toi et tes enfants, selon tout ce que je te commande aujourd'hui;
3 a sa’an nan ne Ubangiji Allahnku zai yi muku jinƙai, yă ji tausayinku, yă kuma sāke tattara ku daga dukan al’ummai inda ya warwatsa ku.
Alors l'Éternel ton Dieu ramènera tes captifs et aura compassion de toi, et il te rassemblera de nouveau d'entre tous les peuples parmi lesquels l'Éternel ton Dieu t'aura dispersé.
4 Ko da ma an kore ku zuwa ƙasa mafi nisa a ƙarƙashin sammai, daga can Ubangiji Allahnku zai tattara ku, yă dawo da ku.
Quand tes dispersés seraient au bout des cieux, de là l'Éternel ton Dieu te rassemblera, et de là il te retirera.
5 Zai dawo da ku zuwa ƙasar da take ta kakanninku, za ku kuwa mallake ta. Zai sa ku yi arziki, ku kuma yi yawa fiye da kakanninku.
Et l'Éternel ton Dieu te ramènera au pays que possédèrent tes pères, et tu le posséderas; il te fera du bien, et te multipliera plus que tes pères.
6 Ubangiji Allahnku zai yi wa zukatanku kaciya da kuma zukatan zuriyarku, saboda ku ƙaunace shi da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, ku kuma rayu.
Et l'Éternel ton Dieu circoncira ton cœur, et le cœur de ta postérité, pour que tu aimes l'Éternel ton Dieu de tout ton cœur et de toute ton âme, afin que tu vives.
7 Ubangiji Allahnku zai sa dukan waɗannan la’anoni a kan abokan gābanku waɗanda suke ƙinku, suke kuma tsananta muku.
Et l'Éternel ton Dieu mettra toutes ces imprécations sur tes ennemis, et sur ceux qui te haïssent et qui t'auront persécuté.
8 Za ku sāke yi wa Ubangiji biyayya, ku kuma bi dukan umarnan da nake ba ku a yau.
Mais toi, tu te convertiras, et tu obéiras à la voix de l'Éternel, et tu pratiqueras tous ses commandements que je te prescris aujourd'hui.
9 Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai mayar da ku masu arziki ƙwarai a cikin dukan aiki hannuwanku, da kuma cikin’ya’yanku, da’ya’yan shanunku, da kuma hatsin gonarku. Ubangiji zai sāke jin daɗinku yă sa ku yi arziki, kamar dai yadda ya ji daɗin kakanninku.
Et l'Éternel ton Dieu te fera abonder en biens dans toutes les œuvres de ta main, dans le fruit de tes entrailles, dans le fruit de ton bétail et dans le fruit de ton sol; car l'Éternel prendra de nouveau plaisir à te faire du bien, comme il y a pris plaisir pour tes pères,
10 In dai kuka yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma kiyaye umarnansa da ƙa’idodin da aka rubuta a wannan Littafin Doka, kuka juyo ga Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
Quand tu obéiras à la voix de l'Éternel ton Dieu, pour garder ses commandements et ses statuts écrits dans ce livre de la loi; quand tu te convertiras à l'Éternel ton Dieu de tout ton cœur et de toute ton âme.
11 To, abin da nake umartanku a yau, ba mai wuya ba ne gare ku, ba kuma abin da ya fi ƙarfinku ba ne.
Car ce commandement que je te prescris aujourd'hui n'est point trop élevé au-dessus de toi, et n'est pas éloigné.
12 Ba ya can sama, balle ku ce, “Wa zai hau sama yă kawo mana, yă kuma furta mana, don mu yi biyayya?”
Il n'est pas dans les cieux, pour qu'on dise: Qui montera pour nous aux cieux, et nous l'apportera, et nous le fera entendre, pour que nous le pratiquions?
13 Ba kuwa yana gaba da teku ba, da za ku ce, “Wa zai haye tekun don yă kawo mana, yă kuma furta mana, don mu yi biyayya?”
Il n'est point non plus au delà de la mer, pour qu'on dise: Qui passera pour nous au delà de la mer, et nous l'apportera, et nous le fera entendre, pour que nous le pratiquions?
14 A’a, kalmar tana nan dab da ku, tana cikin bakinku da cikin zuciyarku, don ku yi biyayya.
Car cette parole est fort près de toi, dans ta bouche et dans ton cœur, afin que tu l'accomplisses.
15 Ku duba, na sa a gabanku a yau, rai da wadata, mutuwa da kuma hallaka.
Regarde, j'ai mis aujourd'hui devant toi la vie et le bien, la mort et le mal.
16 Gama na umarce ku a yau, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, don ku yi tafiya a hanyoyinsa, ku kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa da kuma dokokinsa, sa’an nan za ku rayu, ku kuma ƙaru, Ubangiji Allahnku kuwa zai albarkace ku a ƙasar da kuke shiga don ci gādonta.
Car je te commande aujourd'hui d'aimer l'Éternel ton Dieu, de marcher dans ses voies, et d'observer ses commandements, ses statuts et ses ordonnances, afin que tu vives, et que tu multiplies, et que l'Éternel ton Dieu te bénisse, au pays où tu vas pour le posséder.
17 Amma in zukatanku suka kangare, ba su kuwa yi biyayya ba, in kuma aka rinjaye ku don ku rusuna ga waɗansu alloli ku yi musu bauta,
Mais si ton cœur se détourne, et que tu n'obéisses pas, et que tu te laisses aller à te prosterner devant d'autres dieux et à les servir,
18 na furta muku yau cewa tabbatacce za a hallaka ku. Ba za ku zauna a ƙasar da kuke hayewa Urdun don ku shiga ku ci gādonta ba.
Je vous déclare aujourd'hui que vous périrez certainement; vous ne prolongerez point vos jours sur la terre où tu vas entrer en passant le Jourdain, pour la posséder.
19 A wannan rana na kira bisa sama da ƙasa a matsayin shaidu a kanku, cewa na sa a gabanku rai da mutuwa, albarku da la’anoni. Yanzu sai ku zaɓi rai, saboda ku da’ya’yanku ku rayu
Je prends aujourd'hui les cieux et la terre à témoin contre vous, que j'ai mis devant toi la vie et la mort, la bénédiction et la malédiction. Choisis donc la vie, afin que tu vives, toi et ta postérité,
20 don kuma ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku saurari muryarsa, ku kuma manne masa. Gama Ubangiji shi ranku, zai kuwa ba ku shekaru masu yawa a ƙasar da ya rantse zai ba wa kakanninku, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.
En aimant l'Éternel ton Dieu, en obéissant à sa voix, et en demeurant attaché à lui; car c'est lui qui est ta vie et la longueur de tes jours; en sorte que tu habites sur le sol que l'Éternel a juré de donner à tes pères, Abraham, Isaac et Jacob.

< Maimaitawar Shari’a 30 >