< Maimaitawar Shari’a 30 >

1 Sa’ad da dukan albarku da la’anonin nan da na sa a gabanku suka zo muku, kuka kuma sa su a zuciya, a duk inda Ubangiji Allahnku ya watsar da ku a cikin al’ummai,
One day after you experience all this, the blessings and curses I've told you about, you'll think about them, living in all the different nations where the Lord your God has exiled you.
2 sa’ad da kuma ku da’ya’yanku kuka komo ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi biyayya da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, bisa ga kome da na umarce ku a yau,
When that happens, and when you and your children come back to the Lord your God, and when you do what he says with all your mind and all your being in accordance with everything I'm telling you today, then the Lord your God will be merciful to you.
3 a sa’an nan ne Ubangiji Allahnku zai yi muku jinƙai, yă ji tausayinku, yă kuma sāke tattara ku daga dukan al’ummai inda ya warwatsa ku.
He will bring you back home, gathering you from all the nations where he scattered you.
4 Ko da ma an kore ku zuwa ƙasa mafi nisa a ƙarƙashin sammai, daga can Ubangiji Allahnku zai tattara ku, yă dawo da ku.
Even if you were exiled to the ends of the earth, will gather you from there and bring you back.
5 Zai dawo da ku zuwa ƙasar da take ta kakanninku, za ku kuwa mallake ta. Zai sa ku yi arziki, ku kuma yi yawa fiye da kakanninku.
The Lord your God will bring you home to the country that belonged to your forefathers and you will own it again. He will make you successful, and you will have even more descendants than your forefathers.
6 Ubangiji Allahnku zai yi wa zukatanku kaciya da kuma zukatan zuriyarku, saboda ku ƙaunace shi da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, ku kuma rayu.
The Lord your God will make you and your descendants his again, and you will love him with all your mind and with all your being, so that you'll live.
7 Ubangiji Allahnku zai sa dukan waɗannan la’anoni a kan abokan gābanku waɗanda suke ƙinku, suke kuma tsananta muku.
Then the Lord your God will place all these curses upon your enemies instead, on those who hate and persecute you.
8 Za ku sāke yi wa Ubangiji biyayya, ku kuma bi dukan umarnan da nake ba ku a yau.
You will once again do what the Lord tells you and follow all his commandments that I'm giving you today.
9 Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai mayar da ku masu arziki ƙwarai a cikin dukan aiki hannuwanku, da kuma cikin’ya’yanku, da’ya’yan shanunku, da kuma hatsin gonarku. Ubangiji zai sāke jin daɗinku yă sa ku yi arziki, kamar dai yadda ya ji daɗin kakanninku.
The Lord your God will make you successful in everything you do, you will have children, your livestock will be productive, and you will have good harvests. The Lord will once again be happy to do you good, as he did to your forefathers,
10 In dai kuka yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma kiyaye umarnansa da ƙa’idodin da aka rubuta a wannan Littafin Doka, kuka juyo ga Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
if you obey the Lord your God by keeping his commandments and regulations written in this book of the Law, and if you come back to him with all your mind and with all your being.
11 To, abin da nake umartanku a yau, ba mai wuya ba ne gare ku, ba kuma abin da ya fi ƙarfinku ba ne.
The instruction I'm giving you today isn't too difficult for you to follow. It's not as if it's so far from you that it's impossible to achieve.
12 Ba ya can sama, balle ku ce, “Wa zai hau sama yă kawo mana, yă kuma furta mana, don mu yi biyayya?”
It's not in heaven so you have to ask, “Who is going to go up to heaven get it for us and let us know what it says so we can obey it?”
13 Ba kuwa yana gaba da teku ba, da za ku ce, “Wa zai haye tekun don yă kawo mana, yă kuma furta mana, don mu yi biyayya?”
It's not across the ocean not beyond the sea so you have to ask, “Who is going to cross the ocean to get it for us and let us know what it says so we can obey it?”
14 A’a, kalmar tana nan dab da ku, tana cikin bakinku da cikin zuciyarku, don ku yi biyayya.
No—you have this instruction is right there with you. It's in your mouth and in your mind so you can obey it.
15 Ku duba, na sa a gabanku a yau, rai da wadata, mutuwa da kuma hallaka.
Listen! Today I've placed a choice before you: life and what's good, or death and what's evil.
16 Gama na umarce ku a yau, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, don ku yi tafiya a hanyoyinsa, ku kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa da kuma dokokinsa, sa’an nan za ku rayu, ku kuma ƙaru, Ubangiji Allahnku kuwa zai albarkace ku a ƙasar da kuke shiga don ci gādonta.
I'm telling you today to love the Lord your God, to follow his ways, and to keep his commandments, rules, and regulations, so you can live and grow in number, and so the Lord your God may bless you in the country that you are entering and will own.
17 Amma in zukatanku suka kangare, ba su kuwa yi biyayya ba, in kuma aka rinjaye ku don ku rusuna ga waɗansu alloli ku yi musu bauta,
If you disregard this and you refuse to listen, if you're lured into bowing down to other gods and worshiping them,
18 na furta muku yau cewa tabbatacce za a hallaka ku. Ba za ku zauna a ƙasar da kuke hayewa Urdun don ku shiga ku ci gādonta ba.
then I warn you right now that you will definitely die. You won't live long in the country that you're going to own after you cross the Jordan.
19 A wannan rana na kira bisa sama da ƙasa a matsayin shaidu a kanku, cewa na sa a gabanku rai da mutuwa, albarku da la’anoni. Yanzu sai ku zaɓi rai, saboda ku da’ya’yanku ku rayu
I call on heaven and earth to be my witnesses against you today that I have placed before you life and death, blessings and curses. Choose life, so you and your descendants will live,
20 don kuma ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku saurari muryarsa, ku kuma manne masa. Gama Ubangiji shi ranku, zai kuwa ba ku shekaru masu yawa a ƙasar da ya rantse zai ba wa kakanninku, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.
so you will love the Lord your God, obey him, and hold onto him. For he is your life, and he will give you long lives in the country that the Lord promised to give your forefathers, to Abraham, Isaac, and Jacob.

< Maimaitawar Shari’a 30 >