< Maimaitawar Shari’a 30 >

1 Sa’ad da dukan albarku da la’anonin nan da na sa a gabanku suka zo muku, kuka kuma sa su a zuciya, a duk inda Ubangiji Allahnku ya watsar da ku a cikin al’ummai,
“Now when all these things will have fallen over you, the blessing or the curse that I have set forth in your sight, and you will have been led to repentance in your heart among all the nations to which the Lord your God will have dispersed you,
2 sa’ad da kuma ku da’ya’yanku kuka komo ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi biyayya da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, bisa ga kome da na umarce ku a yau,
and when you will have returned to him, so as to obey his commandments, just as I have instructed you this day, with your sons, with your whole heart and with your whole soul,
3 a sa’an nan ne Ubangiji Allahnku zai yi muku jinƙai, yă ji tausayinku, yă kuma sāke tattara ku daga dukan al’ummai inda ya warwatsa ku.
then the Lord your God will lead you away from your captivity, and he will take pity on you, and he will gather you again from all the nations to which he had dispersed you before.
4 Ko da ma an kore ku zuwa ƙasa mafi nisa a ƙarƙashin sammai, daga can Ubangiji Allahnku zai tattara ku, yă dawo da ku.
Even if you will have been scattered as far as the poles of the heavens, the Lord your God will retrieve you from there.
5 Zai dawo da ku zuwa ƙasar da take ta kakanninku, za ku kuwa mallake ta. Zai sa ku yi arziki, ku kuma yi yawa fiye da kakanninku.
And he will take you up and lead you into the land which your fathers had possessed, and you shall obtain it. And in blessing you, he will make you greater in number than your fathers ever were.
6 Ubangiji Allahnku zai yi wa zukatanku kaciya da kuma zukatan zuriyarku, saboda ku ƙaunace shi da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, ku kuma rayu.
The Lord your God will circumcise your heart, and the heart of your offspring, so that you may love the Lord your God with your entire heart and with your entire soul, so that you may be able to live.
7 Ubangiji Allahnku zai sa dukan waɗannan la’anoni a kan abokan gābanku waɗanda suke ƙinku, suke kuma tsananta muku.
And he will turn all these curses upon your enemies, and upon those who hate and persecute you.
8 Za ku sāke yi wa Ubangiji biyayya, ku kuma bi dukan umarnan da nake ba ku a yau.
But you shall return, and you shall listen to the voice of the Lord your God. And you shall carry out all the commandments which I am entrusting to you this day.
9 Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai mayar da ku masu arziki ƙwarai a cikin dukan aiki hannuwanku, da kuma cikin’ya’yanku, da’ya’yan shanunku, da kuma hatsin gonarku. Ubangiji zai sāke jin daɗinku yă sa ku yi arziki, kamar dai yadda ya ji daɗin kakanninku.
And the Lord your God will cause you to abound in all the works of your hands, in the progeny of your womb, and in the fruit of your cattle, in the fertility of your land, and with an abundance of all things. For the Lord will return, so that he may rejoice over you in all good things, just as he rejoiced in your fathers:
10 In dai kuka yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma kiyaye umarnansa da ƙa’idodin da aka rubuta a wannan Littafin Doka, kuka juyo ga Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
but only if you will listen to the voice of the Lord your God, and keep his precepts and ceremonies, which have been written in this law, and only if you return to the Lord your God with all your heart and with all your soul.
11 To, abin da nake umartanku a yau, ba mai wuya ba ne gare ku, ba kuma abin da ya fi ƙarfinku ba ne.
This commandment, which I entrust to you today, is not high above you, nor has it been placed far away.
12 Ba ya can sama, balle ku ce, “Wa zai hau sama yă kawo mana, yă kuma furta mana, don mu yi biyayya?”
Nor is it in heaven, so that you would be able to say, ‘Which of us can ascend to heaven, so as to carry it back to us, and so that we may hear it and fulfill it in deed?’
13 Ba kuwa yana gaba da teku ba, da za ku ce, “Wa zai haye tekun don yă kawo mana, yă kuma furta mana, don mu yi biyayya?”
Nor is it beyond the sea, so that you would excuse yourself by saying, ‘Which of us is able to cross the sea, and to carry it back to us, so that we may be able to hear and to do what has been instructed?’
14 A’a, kalmar tana nan dab da ku, tana cikin bakinku da cikin zuciyarku, don ku yi biyayya.
Instead, the word is near to you, in your mouth and in your heart, so that you may do it.
15 Ku duba, na sa a gabanku a yau, rai da wadata, mutuwa da kuma hallaka.
Consider what I have set forth in your sight this day, life and good, or, on the opposite side, death and evil,
16 Gama na umarce ku a yau, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, don ku yi tafiya a hanyoyinsa, ku kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa da kuma dokokinsa, sa’an nan za ku rayu, ku kuma ƙaru, Ubangiji Allahnku kuwa zai albarkace ku a ƙasar da kuke shiga don ci gādonta.
so that you may love the Lord your God, and walk in his ways, and keep his commandments and ceremonies and judgments, and so that you may live, and he may multiply you and bless you in the land, which you shall enter in order to possess.
17 Amma in zukatanku suka kangare, ba su kuwa yi biyayya ba, in kuma aka rinjaye ku don ku rusuna ga waɗansu alloli ku yi musu bauta,
But if your heart will have been turned aside, so that you are not willing to listen, and, having been deceived by error, you adore strange gods and serve them,
18 na furta muku yau cewa tabbatacce za a hallaka ku. Ba za ku zauna a ƙasar da kuke hayewa Urdun don ku shiga ku ci gādonta ba.
then I predict to you this day that you will perish, and you will remain for only a short time in the land, for which you shall cross the Jordan, and which you shall enter in order to possess.
19 A wannan rana na kira bisa sama da ƙasa a matsayin shaidu a kanku, cewa na sa a gabanku rai da mutuwa, albarku da la’anoni. Yanzu sai ku zaɓi rai, saboda ku da’ya’yanku ku rayu
I call heaven and earth as witnesses this day, that I have set before you life and death, blessing and curse. Therefore, choose life, so that both you and your offspring may live,
20 don kuma ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku saurari muryarsa, ku kuma manne masa. Gama Ubangiji shi ranku, zai kuwa ba ku shekaru masu yawa a ƙasar da ya rantse zai ba wa kakanninku, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.
and so that you may love the Lord your God, and obey his voice, and cling to him, (for he is your life and the length of your days) and so that you may live in the land, about which the Lord swore to your fathers, Abraham, Isaac, and Jacob, that he would give it to them.”

< Maimaitawar Shari’a 30 >