< Maimaitawar Shari’a 30 >
1 Sa’ad da dukan albarku da la’anonin nan da na sa a gabanku suka zo muku, kuka kuma sa su a zuciya, a duk inda Ubangiji Allahnku ya watsar da ku a cikin al’ummai,
Og det skal ske, naar alle disse Ting komme over dig, Velsignelsen og Forbandelsen, som jeg har lagt for dit Ansigt, og du tager det igen til Hjerte iblandt alle Hedningerne, der, hvorhen Herren din Gud har fordrevet dig;
2 sa’ad da kuma ku da’ya’yanku kuka komo ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi biyayya da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, bisa ga kome da na umarce ku a yau,
og du omvender dig til Herren din Gud, og du hører hans Røst, aldeles som jeg byder dig i Dag, du og dine Børn, af dit ganske Hjerte og af din ganske Sjæl;
3 a sa’an nan ne Ubangiji Allahnku zai yi muku jinƙai, yă ji tausayinku, yă kuma sāke tattara ku daga dukan al’ummai inda ya warwatsa ku.
da skal Herren din Gud vende dit Fangenskab og forbarme sig over dig og atter samle dig fra alle de Folk, til hvilke Herren din Gud havde bortspredt dig.
4 Ko da ma an kore ku zuwa ƙasa mafi nisa a ƙarƙashin sammai, daga can Ubangiji Allahnku zai tattara ku, yă dawo da ku.
Om nogen af dig var fordreven til Himmelens Ende, skal Herren din Gud samle dig derfra og tage dig derfra.
5 Zai dawo da ku zuwa ƙasar da take ta kakanninku, za ku kuwa mallake ta. Zai sa ku yi arziki, ku kuma yi yawa fiye da kakanninku.
Og Herren din Gud skal føre dig til det Land, som dine Fædre ejede, og du skal eje det, og han skal gøre vel imod dig og formere dig mere end dine Fædre.
6 Ubangiji Allahnku zai yi wa zukatanku kaciya da kuma zukatan zuriyarku, saboda ku ƙaunace shi da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, ku kuma rayu.
Og Herren din Gud skal omskære dit Hjerte og dit Afkoms Hjerte, at du skal elske Herren din Gud af dit ganske Hjerte og af din ganske Sjæl, at du maa leve.
7 Ubangiji Allahnku zai sa dukan waɗannan la’anoni a kan abokan gābanku waɗanda suke ƙinku, suke kuma tsananta muku.
Og Herren din Gud skal lægge alle disse Forbandelser paa dine Fjender og paa dem, som hade dig, og som have forfulgt dig.
8 Za ku sāke yi wa Ubangiji biyayya, ku kuma bi dukan umarnan da nake ba ku a yau.
Men du skal omvende dig og høre paa Herrens Røst, og du skal gøre efter alle hans Bud, som jeg byder dig i Dag.
9 Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai mayar da ku masu arziki ƙwarai a cikin dukan aiki hannuwanku, da kuma cikin’ya’yanku, da’ya’yan shanunku, da kuma hatsin gonarku. Ubangiji zai sāke jin daɗinku yă sa ku yi arziki, kamar dai yadda ya ji daɗin kakanninku.
Og Herren din Gud skal give dig Overflod under alle dine Hænders Gerninger af dit Livs Frugt og af dit Kvægs Frugt og af dit Lands Frugt, dig til Gode; thi Herren vil atter glæde sig over dig til det gode, ligesom han glædede sig over dine Fædre,
10 In dai kuka yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma kiyaye umarnansa da ƙa’idodin da aka rubuta a wannan Littafin Doka, kuka juyo ga Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
naar du hører paa Herren din Guds Røst, saa at du holder hans Bud og hans Skikke, det som er skrevet i denne Lovbog; naar du omvender dig til Herren din Gud af dit ganske Hjerte og af din ganske Sjæl.
11 To, abin da nake umartanku a yau, ba mai wuya ba ne gare ku, ba kuma abin da ya fi ƙarfinku ba ne.
Thi dette Bud, som jeg byder dig i Dag, det er ikke underligt for dig, det er ej heller langt borte.
12 Ba ya can sama, balle ku ce, “Wa zai hau sama yă kawo mana, yă kuma furta mana, don mu yi biyayya?”
Det er ikke i Himmelen, at du maatte sige: Hvo vil fare os op til Himmelen og hente os det og lade os høre det, at vi maa gøre derefter?
13 Ba kuwa yana gaba da teku ba, da za ku ce, “Wa zai haye tekun don yă kawo mana, yă kuma furta mana, don mu yi biyayya?”
Det er ej heller paa hin Side Havet, at du maatte sige: Hvo vil fare os over paa hin Side Havet og hente os det og lade os høre det, at vi maa gøre derefter?
14 A’a, kalmar tana nan dab da ku, tana cikin bakinku da cikin zuciyarku, don ku yi biyayya.
Thi det Ord er saare nær hos dig, i din Mund og i dit Hjerte, at du skal gøre derefter.
15 Ku duba, na sa a gabanku a yau, rai da wadata, mutuwa da kuma hallaka.
Se, jeg har lagt dig for i Dag Livet og det gode og Døden og det onde.
16 Gama na umarce ku a yau, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, don ku yi tafiya a hanyoyinsa, ku kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa da kuma dokokinsa, sa’an nan za ku rayu, ku kuma ƙaru, Ubangiji Allahnku kuwa zai albarkace ku a ƙasar da kuke shiga don ci gādonta.
Thi jeg byder dig i Dag at elske Herren din Gud, at vandre i hans Veje og at holde hans Bud og hans Skikke og hans Befalinger, at du maa leve og formeres, og Herren din Gud maa velsigne dig i det Land, som du kommer hen til for at eje det.
17 Amma in zukatanku suka kangare, ba su kuwa yi biyayya ba, in kuma aka rinjaye ku don ku rusuna ga waɗansu alloli ku yi musu bauta,
Men dersom dit Hjerte vender sig bort, og du ikke hører, men lader dig forføre, saa at du tilbeder andre Guder og tjener dem:
18 na furta muku yau cewa tabbatacce za a hallaka ku. Ba za ku zauna a ƙasar da kuke hayewa Urdun don ku shiga ku ci gādonta ba.
Da forkynder jeg eder i Dag, at I skulle omkomme; I skulle ikke forlænge eders Dage i Landet, til hvilket du drager over Jordanen for at komme derhen til at eje det.
19 A wannan rana na kira bisa sama da ƙasa a matsayin shaidu a kanku, cewa na sa a gabanku rai da mutuwa, albarku da la’anoni. Yanzu sai ku zaɓi rai, saboda ku da’ya’yanku ku rayu
Jeg tager i Dag Himmelen og Jorden til Vidne mod eder, at jeg har forelagt dig Livet og Døden, Velsignelsen og Forbandelsen, at du maa udvælge Livet, paa det du maa leve, du og din Sæd,
20 don kuma ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku saurari muryarsa, ku kuma manne masa. Gama Ubangiji shi ranku, zai kuwa ba ku shekaru masu yawa a ƙasar da ya rantse zai ba wa kakanninku, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.
at du maa elske Herren din Gud og høre paa hans Røst og hænge ved ham; thi han er dit Liv og dine Dages Længde; at du maa blive i Landet, som Herren tilsvor dine Fædre, Abraham, Isak og Jakob, at give dem.