< Maimaitawar Shari’a 3 >
1 Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
И обратившеся взыдохом путем иже к Васану: и изыде Ог царь Васанский противу нам, сам и вси людие его с ним на брань во Едраим.
2 Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
И рече Господь ко мне: не убойся его, яко в руце твои предах его, и вся люди его, и всю землю его: и сотвориши ему, якоже сотворил еси Сиону царю Аморрейску, иже живяше во Есевоне.
3 Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
И предаде его Господь Бог наш в руце наши, и Ога царя Васанска, и вся люди его: и избихом его, дондеже не остася от него семя:
4 A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
и одержахом вся грады его во время оно, не бысть града, егоже не взяхом от них: шестьдесят градов, вся пределы Аргова царя Ога в Васане,
5 Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
вся грады тверды, стены высоки, врата и вереи, кроме градов ферезейских многих зело:
6 Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
потребихом их, якоже сотворихом Сиону царю Есевоню, и потребихом вся грады, вкупе и жены их и чада:
7 Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
и вся скоты, и корысти градныя пленихом себе,
8 A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
и взяхом в то время землю от рук двух царей Аморрейских, иже быша об оны пол Иордана, от водотечи Арнони, даже и до горы Аермона.
9 (Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
Финикиане прозывают Аермон Саниором, Аморрей же прозва его Саниром.
10 Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
Вси грады мисоровы, и весь Галаад, и весь Васан даже до Елхи и Едраима, грады царствия Огова в Васане:
11 (Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
яко точию Ог царь Васанский остася от Рафаинов: се, одр его одр железен, се, той есть в Краеградии сынов Аммановых: девять лакот долгота его и четыри лакти широта его лактем мужеским.
12 Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
И землю ту наследихом во оно время от Ароира, иже есть у устия водотечи Ариони, и пол горы Галаадовы: и грады его дах Рувиму и Гаду:
13 Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
и оставшее Галаадово, и все Васанское царство Огово дах полуплемени Манассиину, и весь предел Аргова, весь Васан оный, земля Рафаиня вменится.
14 Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
И Иаир сын Манассиин взя вся пределы Аргова, даже до предел Гаргасинских и Махафинских: прозва я по имени своему Васан Авоф Иаир, даже до сего дне:
15 Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
и Махиру дах Галаад,
16 Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
и Рувиму и Гадови дах от Галаада даже до водотечи Арнони, среди водотечи предел, и даже до Иавока: водотеча предел сынов Амманих:
17 Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
и арава и Иордан предел от Махенерефа и даже до моря Аравскаго, моря Сланаго, под асидофом Фазги от востока.
18 Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
И повелех вам во время оно, глаголя: Господь Бог ваш даде вам землю сию во жребий: вооружени поидите пред лицем братии вашея сынов Израилевых, всяк сильный:
19 Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
точию жены вашя и дети вашя и скоти вашя, вем, яко скот мног есть вам, да пребудут во градех ваших, яже дах вам:
20 sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
дондеже упокоит Господь Бог наш братию вашу, якоже и вас, и наследят и сии землю, юже Господь Бог ваш дает им об ону страну Иордана: и возвратитеся кийждо в наследие свое иже дах вам.
21 A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
И Иисусу заповедах во время оно, глаголя: очи ваши видеша вся, елика сотвори Господь Бог наш обоим царем сим, тако сотворит Господь Бог наш всем царством, ихже сквозе ты пройдеши тамо:
22 Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
не убойтеся от них, яко Господь Бог наш Сам поборет по вас.
23 A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
И молихся Господви во оно время, глаголя:
24 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
Господи Боже, Ты начал еси показовати Твоему рабу крепость Твою и силу Твою, и руку крепкую и мышцу высокую: кто бо есть бог на небеси или на земли, иже сотворит, якоже сотворил еси Ты, и по крепости Твоей?
25 Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
Прешед убо увижду землю благую сию, яже об ону страну Иордана, гору сию благу и Антиливан.
26 Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
И презре мя Господь вас ради, и не послуша мене, и рече Господь ко Мне: довлеет ти, не приложи к сему глаголати словесе сего:
27 Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
взыди на верх горы Изсеченыя и воззри очима твоима к морю и северу, и югу и на востоки, и виждь очима твоима, яко не прейдеши Иордана сего:
28 Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
и заповеждь Иисусу, и укрепи его, и утеши его: яко сей прейдет пред лицем людий сих, и сей разделит им в наследие всю землю, юже еси видел.
29 Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.
И пребыхом во юдоли близ дому Фогорова.