< Maimaitawar Shari’a 3 >
1 Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
Så tok vi på en annen kant og drog op på veien til Basan; da drog Og, kongen i Basan, og hele hans folk ut mot oss til strid, til Edre'i.
2 Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
Og Herren sa til mig: Frykt ikke for ham! For jeg har gitt ham og hele hans folk og hans land i din hånd, og du skal gjøre med ham som du gjorde med Sihon, amorittenes konge, som bodde i Hesbon.
3 Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
Så gav Herren vår Gud også Og, kongen i Basan, og hele hans folk i vår hånd; og vi slo ham så vi ikke lot nogen bli tilbake eller slippe unda.
4 A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
Og vi inntok dengang alle hans byer; der var ikke en by uten at vi tok den fra dem, seksti byer, hele Argob-landet, Ogs rike i Basan.
5 Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
Alle disse var faste byer med høie murer, dobbelte porter og bommer, foruten en stor mengde landsbyer.
6 Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
Og vi slo dem med bann, som vi hadde gjort med Sihon, kongen i Hesbon; hver by slo vi med bann, menn, kvinner og barn.
7 Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
Men alt feet og hærfanget fra byene tok vi til bytte.
8 A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
Således tok vi dengang landet fra begge amoritterkongene på denne side av Jordan, fra Arnon-åen like til fjellet Hermon -
9 (Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
sidonierne kaller Hermon Sirjon, og amorittene kaller det Senir -
10 Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
alle byene på sletten og hele Gilead og hele Basan like til byene Salka og Edre'i i Ogs rike i Basan;
11 (Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
for Og, kongen i Basan, var den siste som var tilbake av refa'ittene; hans seng, som er av jern, står, som alle vet, i ammonitterbyen Rabba; den er ni alen lang og fire alen bred, alnen regnet efter lengden av en manns underarm.
12 Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
Dette land inntok vi dengang: Bygdene fra Aroer, som ligger ved Arnon-åen, og halvdelen av Gileadfjellene med byene der gav jeg til rubenittene og gadittene,
13 Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
og resten av Gilead og hele Basan, Ogs rike, gav jeg til den halve Manasse stamme, hele Argob-landet, hele Basan; det er det som kalles refa'ittenes land.
14 Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
Ja'ir, Manasses sønn, inntok hele Argob-landet like til gesurittenes og ma'akatittenes landemerker, og dette land - Basan-landet - kalte han efter sitt eget navn Ja'irs byer, og så har det hett til denne dag.
15 Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
Og til Makir gav jeg Gilead.
16 Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
Og til rubenittene og gadittene gav jeg landet fra Gilead til Arnon-åen, til midt i åen, og landet langsmed den, og til Jabbok-åen, Ammons barns grense,
17 Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
og ødemarken og Jordan og landet langsmed den, fra Kinnerets sjø til Ødemarks-havet - Salthavet - nedenfor Pisga-liene, mot øst.
18 Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
Dengang bød jeg eder og sa: Herren eders Gud har gitt eder dette land til eie; væbnet skal I, alle som er krigsdyktige menn, dra frem foran eders brødre, Israels barn.
19 Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
Bare eders hustruer og barn og eders fe - jeg vet at I har meget fe - skal bli igjen i de byer jeg har gitt eder,
20 sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
inntil Herren gir eders brødre ro likesom eder, og de og har tatt det land i eie som Herren eders Gud gir dem på hin side Jordan; da kan I vende tilbake, hver til den eiendom jeg har gitt eder.
21 A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
På samme tid bød jeg Josva og sa: Du har med egne øine sett alt det Herren eders Gud har gjort med disse to konger; således vil Herren gjøre med alle de riker du drar over til.
22 Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
I skal ikke være redde for dem; for Herren eders Gud vil selv stride for eder.
23 A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
For jeg bønnfalt dengang Herren og sa:
24 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
Herre, Herre! Du har begynt å la din tjener se din storhet og din sterke hånd; for hvor er det en gud i himmelen og på jorden som kan gjøre sådanne gjerninger og storverk som du?
25 Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
La mig nu få dra over og se det gode land på hin side Jordan, dette gode fjell-land og Libanon!
26 Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
Men Herren var vred på mig for eders skyld, og han hørte ikke på mig, men han sa til mig: La det nu være nok, tal ikke mere til mig om dette!
27 Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
Gå op på Pisgas topp og løft dine øine mot vest og mot nord og mot syd og mot øst, og se vidt omkring dig! For over Jordan her skal du ikke komme.
28 Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
Og gi Josva befaling og gjør ham frimodig og sterk! For han skal føre dette folk over, og han skal gi dem til arv det land du skal skue.
29 Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.
Så blev vi da i dalen midt imot Bet-Peor.