< Maimaitawar Shari’a 3 >

1 Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
Aa le nitolike tika nionjoñe amy lala­ñey mb’e Basane mb’eo vaho nia­votse hiatrek’ antika t’i Oge mpanjaka’ i Basane, ie naho ondati’e iabio, hialy Edrey.
2 Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
Hoe t’Iehovà amako, Ko ihem­baña’o fa natoloko am-pità’o naho on­dati’e iabio vaho o tane’eo. Ano ama’e hambañe amy nanoe’o i Sihone, mpanjaka’ i Amore nimoneñe e Khesboney.
3 Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
Aa le natolo’ Iehovà Andrianañaharentika am-pitàn-tika ka t’i Oge mpanjaka’ i Basane naho ondati’e iabio, le rinotsan-tika vaho tsy nengan-tsehanga’e.
4 A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
Ie amy zay, tinavan-tika o rova’e iabio; le tsy teo ty rova’e tsy tinavan-tika—rova enempolo, ze hene tane’ i Argobe, ty fifehea’ i Oge e Basane ao.
5 Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
Songa narovañe an-kijoly abo o rovao, lalambey naho sikadañe, tovo’ irezay o tanàñe tsi-fotofoto tsy aman-kijolio.
6 Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
Fonga binaibain-tika hambañe ami’ty nanoan-tika i Sihone mpanjaka’ i Khesbone, songa zinaman-tika ze lahilahy naho rakemba vaho keleiañe amy ze rova iaby.
7 Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
Fe hene rinamben-tika ze añombe naho vara amo rovao ho tsindroke.
8 A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
Le tinavan-tika boak’am-pitàm-panjaka nte-Amore roe amy andro zay ty tane alafe’ Iardeney atoy mifototse amy saka Arnoney pak’ am-bohi-Kermone añe;
9 (Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
(Atao’ o nte-Tsidoneo ty hoe Sirione ty Kermone, le atao’ o nte-Amoreo ty hoe Senire; )
10 Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
le ze rova an-tanemira ey, naho i Gilàde iaby le i Basane iaby, pake Salkà añe vaho i Edrey, o rova am-pifehea’ i Oge nte-Basaneo.
11 (Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
I Oge mpanjaka’ i Basane ty ni-sengaha’ o fanalolahio; inao te fandream-by ty fandrea’e, mbe e Rabate ao izay amo ana’ i Amoneo. Sive kiho ty an-dava’e naho efatse kiho ty ampohe’e an-kiho tsotra.
12 Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
Le natoloko amo nte-Reobeneo naho amo nte-Gadeo i tane rinamben-tika amy andro zaiy, boak’ Aroere añ’ olo’ i saka Arnoney naho ty tampa’ i Vohi-Gilàdey, naho o rova’eo.
13 Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
Le natoloko amy vakim-pifokoa’ i Menasèy ty sisa’ i Gilade naho i Basane iaby, toe ty fifehea’ i Oge, le nitokaveñe ty hoe tanem-panalolahy ze hene tane’ i Argobe mitraoke amy Basane iaby.
14 Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
Iaire ana’ i Menasè ty nandrambe ty tane’i Argobe pak’añ’olo’ i Gesory naho i Maàkaty añe vaho nito­kave’e amy tahina’ey ty hoe: Basane-kavote-Iaire pake henane.
15 Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
Le natoloko amy Makire ty Gilade.
16 Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
Le natoloko amo nte-Reobeneo naho amo nte-Gadeo ty tane boake Gilade pak’ an-tsaka’ Arnone, ty aivo’ i vavataney ro efe’e, pak’ an-tsaka’ Iabòke eo, ty efe-tane’ o ana’ i Amoneo;
17 Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
naho i tane Mìray, Iardeney ty efe’e, le boak’e Kinerete pak’ an-dria’ i antanemira, i ria-tsiray, am-potom-piroroña’ i Asdote-Pisgà maniñanañe.
18 Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
Le hoe ty nandiliako anahareo henane zay: Fa natolo’ Iehovà Andrianañahare’ areo ho fanaña’ areo o tane atoio le hitsake reke-pialiañe aolo’ o rahalahi’ areo ana’ Israeleo ze mahatan-defo ama’ areo iaby.
19 Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
Fe hidoñe amo rova natoloko anahareoo o vali’ areoo, o keleia’ areoo, naho o añombe’ areoo (apotako te maro ty añombe’ areo);
20 sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
aa naho nampitofà’ Iehovà manahak’ anahareo o rahalahi’ areoo, naho fa nitobea’ iareo ka ty tane natolo’ Iehovà Andrianañahare’ areo alafe’ Iardeney añe, izay vaho himpoly nahareo—ze fonga ondaty—mb’ an-tane’e mb’eo, i natoloko anahareoy.
21 A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
Le nafantoko am’ Iehosoa amy andro zay ty hoe, Toe hene nioni-pihaino’o ty nanoe’ Iehovà Andrianañahare’o i mpanjaka roe rey, le izay ka ty hanoe’ Iehovà ze fifeheañe irangà’ areo.
22 Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
Ko ihembaña’ areo fa Iehovà Andrianañahare’ areo ty mialy ho anahareo.
23 A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
Ie amy zay, nihalaly am’ Iehovà iraho ami’ty hoe:
24 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
O Talè Iehovà, ie vaho niorotse nampiboake ty hajabahina’o naho ty haozara’o ami’ty mpitoro’o, le ia ty ndrahare an-dikerañe ao ndra an-tane atoy ty mahafitoloñe hambañe amo anoe’oo naho o sata’o ra’elahio?
25 Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
Ehe te henga’o hitsake mb’eo iraho hahatreavako i tane fanjaka alafe’ Iardene añey, o vohibohitse soao naho i Lebanone.
26 Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
F’ie niviñera’ Iehovà ty ama’ areo le tsy ni­haoñe’e. Hoe t’Iehovà amako, Fa eneñe i azoy! ko isaontsia’o ka.
27 Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
Miañam­bonea mb’ an-dengo’ i Pisgà mb’eo le miandrà makandrefa naho mañavaratse naho mañatimo naho maniñanañe eñe. Italakeso am-pihaino, f’ie tsy hitsake Iardeney.
28 Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
Afantoho t’Iehosoa naho osiho vaho haozaro, amy t’ie ro hitsake hiaolo ondaty retia, le ie ty hampandova iareo o tane ho isa’oo.
29 Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.
Aa le nitamañe am-bavatane tandrife i Bete-piore eo tika.

< Maimaitawar Shari’a 3 >