< Maimaitawar Shari’a 3 >
1 Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
Tad mēs griezāmies un gājām uz augšu pa Basanas ceļu, un Ogs, Basanas ķēniņš, mums gāja pretī, pats ar visiem saviem ļaudīm, karot pie Edrejas.
2 Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
Un Tas Kungs sacīja uz mani: nebīsties no viņa, jo Es viņu un visus viņa ļaudis un viņa zemi esmu devis tavā rokā, un tev būs viņam darīt, tā tu esi darījis Sihonam, Amoriešu ķēniņam, kas dzīvoja Hešbonā.
3 Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
Un Tas Kungs, mūsu Dievs, deva mūsu rokā arī Ogu, Basanas ķēniņu, līdz ar visiem viņa ļaudīm, un mēs to sakāvām, kamēr viņam nekas neatlika.
4 A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
Un mēs uzņēmām tanī laikā visas viņa pilsētas; nevienas pilsētas nebija, ko mēs viņam nebūtu atņēmuši; sešdesmit pilsētas, visu Argoba daļu, Oga valsti Basanā.
5 Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
Visas tās pilsētas bija apstiprinātas ar augstiem mūriem, vārtiem un bultām; - bez tam vēl daudz miestus.
6 Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
Un mēs tos izdeldējām, itin kā bijām darījuši Sihonam, Hešbonas ķēniņam, izdeldēdami visas pilsētas, vīrus, sievas un bērniņus.
7 Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
Bet visus lopus un to laupījumu tais pilsētās paņēmām sev.
8 A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
Tā mēs tanī laikā paņēmām to zemi no to divu Amoriešu ķēniņu rokas, viņpus Jardānes, no Arnonas upes līdz Hermona kalnam,
9 (Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
(Sidonieši Hermonu sauc par Zirionu, bet Amorieši viņu sauc par Seniru) -
10 Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
Visas pilsētas klajumā un visu Gileādu un visu Basanu līdz Zalkai un Edrejai, Oga valsts pilsētām Basanā.
11 (Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
(Jo Ogs, Basanas ķēniņš, vien bija atlicies no tiem atlikušiem milžiem; redzi, viņa gulta, dzelzs gulta, vai tā nav Ammona bērnu Rabatā? Deviņu olekšu viņas garums un četru olekšu viņas platums, pēc vīra elkoņa.)
12 Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
Tad nu šo zemi tanī laikā ieņēmām no Aroēra, kas ir pie Arnonas upes. Un Gileādas kalnu un viņas pilsētu vienu pusi es atdevu Rūbena un Gada bērniem.
13 Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
Un kas atlikās no Gileādas un visu Basanu, Oga valsti, es atdevu Manasus pusciltij, visu Argoba apgabalu; visu šo Basanu sauc par milžu zemi.
14 Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
Jaīrs, Manasus dēls, dabūja visu Argoba apgabalu, līdz gešuriešu un Maāhatiešu robežām, un viņš Basanu nosauca pēc sava vārda Avot Jaīru līdz šai dienai.
15 Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
Un Mahiram es devu Gileādu.
16 Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
Bet Rūbena un Gada bērniem es no Gileādas devu līdz Arnonas upei to upes ieleju un malu, un līdz Jabokas upei, Ammona bērnu robežai,
17 Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
Un to klajumu un to Jardāni, kas ir par robežu no Ķineretes līdz klajuma ezeram, tai sāls jūrai, apakš Pizgas pakalniem pret rītiem.
18 Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
Un tanī laikā es jums pavēlēju un sacīju: Tas Kungs, jūsu Dievs, jums šo zemi ir devis iemantot, - bet visi, kas ir stipri vīri, ejat apbruņoti savu brāļu, Israēla bērnu, priekšā;
19 Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
Tikai jūsu sievas un jūsu bērniņi un jūsu ganāmais pulks (jo es zinu, ka jums tas ganāmais pulks ir liels), lai paliek jūsu pilsētās, ko es jums esmu devis,
20 sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
Tiekams Tas Kungs dos dusu jūsu brāļiem, itin kā jums, un tie arīdzan iemantos to zemi, ko Tas Kungs, jūsu Dievs, viņiem dos viņpus Jardānes; tad jums ikvienam būs griezties uz savu daļu, ko es jums esmu devis.
21 A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
Es Jozuam pavēlēju tanī laikā un sacīju: tavas acis ir redzējušas visu, ko Tas Kungs, jūsu Dievs, šiem diviem ķēniņiem ir darījis; tā Tas Kungs darīs visām valstīm, uz kurieni tu iesi.
22 Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
Nebīstaties no viņiem, jo Tas Kungs jūsu Dievs, priekš jums karos.
23 A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
Un es lūdzu To Kungu tanī laikā un sacīju:
24 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
Kungs, Dievs, Tu esi iesācis Savam kalpam parādīt Savu augstību un Savu stipro roku, jo kur ir tāds stiprs Dievs debesīs un virs zemes, kas varētu darīt pēc Taviem darbiem un pēc Tava spēka.
25 Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
Ļauj lūdzams man iet pāri un redzēt to labo zemi, kas ir viņpus Jardānes, tos jaukos kalnus un to Lībanu.
26 Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
Bet Tas Kungs jūsu dēļ iekarsa par mani un mani nepaklausīja, un Tas Kungs uz mani sacīja: lai tev ir gan, nerunā vairs uz Mani par šo lietu.
27 Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
Kāp Pizgas kalna galā un pacel savas acis pret vakariem un pret ziemeļiem un pret dienvidiem un pret rītiem, un pārlūko to ar savām acīm, jo tev nebūs iet pār šo Jardāni.
28 Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
Pavēli tad Jozuam un stiprini viņu un iedrošini viņu, jo viņš ies pāri šo ļaužu priekšā un izdalīs viņiem to zemi, ko tu redzēsi.
29 Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.
Un mēs palikām tanī lejā pret Bet-Peoru.