< Maimaitawar Shari’a 3 >
1 Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
C’est pourquoi, étant retournés, nous montâmes par le chemin de Basan; et Og, roi de Bazan, sortit à notre rencontre avec tout son peuple pour combattre à Edraï.
2 Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
Alors le Seigneur me dit: Ne le crains point, parce qu’il a été livré en ta main avec tout son peuple et sa terre; et tu lui feras comme tu as fait à Séhon, roi des Amorrhéens, qui habitait à Hésébon.
3 Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
Le Seigneur notre Dieu livra donc aussi en nos mains Og, roi de Basan, et tout son peuple; nous les battîmes jusqu’à une entière extermination,
4 A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
Dévastant toutes ses cités en un même temps (il n’y eut point de ville qui nous échappât): soixante villes, toute la contrée d’Argob, royaume d’Og en Basan.
5 Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
Toutes les villes étaient fortifiées de murs très hauts, et de portes et de verrous, outre les villes innombrables qui n’avaient point de murs.
6 Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
Et nous détruisîmes ces peuples, comme nous avions fait à Séhon, roi d’Hésébon, détruisant toute ville, les hommes, les femmes et les petits enfants.
7 Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
Mais les bestiaux et les dépouilles des villes, nous les enlevâmes.
8 A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
Nous prîmes donc en ce temps-là la terre des deux rois des Amorrhéens, qui étaient au-delà du Jourdain, depuis le torrent d’Arnon jusqu’à la montagne d’Hermon,
9 (Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
Que les Sidoniens appellent Sarion, et les Amorrhéens Sanir;
10 Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
Toutes les villes qui sont situées dans la plaine, et toute la terre de Galaad et de Basan jusqu’à Selcha et Edraï, villes du royaume d’Og en Basan.
11 (Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
Car le seul Og, roi de Basan, était resté de la race des géants. On montre son lit de fer qui est à Rabbath des enfants d’Ammon, ayant neuf coudées de longueur, et quatre de largeur, selon la mesure de la coudée d’une main d’homme.
12 Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
Ainsi, nous possédâmes en ce temps-là la terre, depuis Aroër qui est sur le bord du torrent d’Arnon, jusqu’au milieu de la montagne de Galaad, et j’en donnai les villes à Ruben et à Gad.
13 Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
Mais le reste de Galaad et tout le Basan du royaume d’Og, je le livrai à la demi-tribu de Manassé, ainsi que toute la contrée d’Argob: or, tout le Basan est appelé terre de géants.
14 Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
Jaïr, fils de Manassé, posséda toute la contrée d’Argob, jusqu’aux frontières de Gessuri et de Machati; et il appela de son nom Basan, Havoth Jaïr, c’est-à-dire bourgs de Jaïr, ce qui a été leur nom jusqu’au présent jour.
15 Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
Je donnai aussi Galaad à Machir.
16 Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
Mais aux tribus de Ruben et de Gad, je donnai de la terre de Galaad jusqu’au torrent d’Arnon, la moitié du torrent et de ses confins jusqu’au torrent de Jéboc, qui est la frontière des enfants d’Ammon;
17 Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
De plus, la plaine du désert, le Jourdain, et les frontières de Cénéreth jusqu’à la mer du désert, qui est la très salée, jusqu’au pied de la montagne de Phasga, contre l’orient.
18 Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
Et je vous ordonnai en ce temps-là, disant: Le Seigneur votre Dieu vous donne cette terre en héritage; tous prêts au combat, précédez vos frères, les enfants d’Israël, vous tous, hommes forts,
19 Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
Sans vos femmes, vos petits enfants et vos bestiaux. Car je sais que vous avez de nombreux troupeaux; or, ils devront demeurer dans les villes que je vous ai livrées,
20 sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
Jusqu’à ce que le Seigneur accorde le repos à vos frères, comme il vous l’a accordé; et qu’ils possèdent, eux-mêmes aussi, la terre qu’il doit leur donner au-delà du Jourdain: alors chacun retournera en sa possession que je lui ai donnée.
21 A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
À Josué aussi j’ai ordonné en ce temps-là, disant: Tes yeux ont vu ce qu’a fait le Seigneur votre Dieu à ces deux rois: c’est ainsi qu’il fera à tous les royaumes dans lesquels tu dois passer.
22 Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
Ne les crains point; car le Seigneur votre Dieu combattra pour vous.
23 A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
Et je priai le Seigneur en ce temps-là, disant:
24 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
Seigneur Dieu, vous avez commencé à montrer à votre serviteur votre grandeur, et votre main très puissante; car il n’est pas d’autre Dieu ou dans le ciel ou sur la terre, qui puisse faire vos œuvres, et être comparé à votre puissance.
25 Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
Je passerai donc, et je verrai cette terre excellente au-delà du Jourdain, et cette belle montagne, et le Liban.
26 Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
Mais le Seigneur, irrité contre moi à cause de vous, ne m’exauça pas, mais il me dit: C’est assez pour toi, ne me parle plus de cela.
27 Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
Monte au sommet de Phasga, et promène tes yeux vers l’occident, et vers l’aquilon, et le midi, et l’orient, et regarde; car tu ne passeras pas le Jourdain.
28 Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
Ordonne à Josué, affermis-le et le fortifie, parce que c’est lui-même qui précédera ce peuple, et qui leur divisera la terre que tu vas voir.
29 Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.
Et nous demeurâmes dans la vallée, contre le temple de Phogor.