< Maimaitawar Shari’a 3 >
1 Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
Et étant partis nous montâmes du côté de Basan; alors vint à notre rencontre Og, Roi de Basan, lui et tout son peuple pour nous attaquer à Edrei.
2 Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
Et l'Éternel me dit: Ne le redoute pas, car je livre entre tes mains, et lui et tout son peuple et son pays, et tu le traiteras comme tu as traité Sihon, Roi des Amoréens, qui résidait à Hesbon.
3 Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
L'Éternel, notre Dieu, livra, donc aussi entre nos mains Og, Roi de Basan, et tout son peuple, et nous le battîmes jusqu'à ne lui laisser aucun réchappé.
4 A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
Et en même temps nous prîmes toutes ses villes; il n'y eut pas une place que nous ne leur enlevâmes, soixante villes, tout le canton d'Argob, royaume de Og en Basan.
5 Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
Toutes ces villes, à l'exception des villes rurales, très nombreuses, étaient munies de hautes murailles, de portes et de barres.
6 Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
Et nous les dévouâmes, comme nous l'avions fait à Sihon, Roi de Hesbon, dévouant toutes villes, hommes, femmes et enfants.
7 Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
Mais nous fîmes notre butin de la totalité du bétail et des dépouilles des villes.
8 A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
C'est ainsi qu'en ce temps-là nous conquîmes le pays sur les deux rois des Amoréens au delà du Jourdain depuis le torrent de l'Arnon jusqu'au mont Hermon
9 (Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
(les Sidoniens donnent à l'Hermon le nom de Sirion et les Amoréens celui de Sénir),
10 Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
toutes les villes de la plaine, et tout Galaad et tout Basan jusqu'à Salcha et Edrei, villes du royaume de Og en Basan.
11 (Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
(Og, Roi de Basan, était le seul survivant du reste des géants; voici, son lit, lit de fer, n'est-il pas à Rabba dans le pays des fils d'Ammon, ayant neuf coudées de longueur et quatre coudées de largeur, coudée d'homme?)
12 Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
Et dans ce temps-là nous conquîmes ce pays depuis Aroër sur l'Arnon. Et la moitié de la montagne de Galaad avec ses villes, je la donnai aux Rubénites et. aux Gadites;
13 Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
et le reste de Galaad et tout Basan, royaume de Og, je le donnai à la demi-Tribu de Manassé, tout le canton d'Argob, Basan tout entier; c'est ce qui s'appelle le pays des géants.
14 Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
Jaïr, fils de Manassé, conquit tout le canton d'Argob jusqu'aux frontières des Gesurites et des Maachathites, et il y donna, à Basan, d'après son nom, le nom de bourgs de Jaïr, jusqu'aujourd'hui.
15 Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
Et à Machir je donnai Galaad.
16 Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
Et aux Rubénites et aux Gadites, je donnai une partie de Galaad et jusqu'au torrent de l'Arnon, ce qui est en dedans du torrent et le territoire adjacent, jusqu'au Jabbok, torrent frontière des fils d'Ammon,
17 Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
et la plaine et le Jourdain et le territoire adjacent depuis Kinnéreth jusqu'à la mer de la plaine, la Mer-Salée, au pied du Pisga, à l'Orient.
18 Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
En ce temps-là je vous donnai ce commandement: L'Éternel, votre Dieu, vous a livré ce pays pour le conquérir. Il faut que vous, tout ce que vous avez de guerriers, vous marchiez armés en tête de vos frères, les fils d'Israël.
19 Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
Vos femmes, vos enfants et vos troupeaux seuls (je sais que vous avez de nombreux troupeaux) resteront dans vos villes que je vous ai données,
20 sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
jusqu'à ce que l'Éternel ait accordé à vos frères le repos comme à vous, et qu'eux aussi aient conquis le pays que l'Éternel, votre Dieu, leur donne au delà du Jourdain; alors vous pourrez chacun de vous revenir dans votre conquête que je vous ai donnée.
21 A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
Et dans ce temps je donnai mes instructions à Josué en ces termes: Tes yeux ont vu tout ce que l'Éternel, votre Dieu, a fait à ces deux Rois: ainsi fera l'Éternel à tous les royaumes que tu vas envahir.
22 Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
Ne les redoutez pas, car l'Éternel, votre Dieu, lui-même combattra pour vous.
23 A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
Et dans ce même temps je fis à l'Éternel cette supplication:
24 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
Seigneur, Éternel, tu as commencé à montrer à ton serviteur ta majesté et ta main puissante; car où est dans les Cieux et sur la terre un Dieu qui fasse rien de pareil à tes œuvres et à tes exploits?
25 Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
Oh! permets aussi que je passe et que je voie ce beau pays de l'autre côté du Jourdain, ces belles montagnes et le Liban!
26 Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
Mais l'Éternel se courrouça contre moi à cause de vous, et Il ne m'exauça pas, et l'Éternel me dit: C'est assez! ne me parle plus de cette affaire.
27 Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
Monte au sommet du Pisga, puis porte tes regards à l'occident et au septentrion et au midi et à l'orient, et contemple de tes yeux; car tu ne passeras pas ce Jourdain.
28 Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
Et laisse tes instructions à Josué, affermis et fortifie-le; car c'est lui qui marchera à la tête de ce peuple, et qui leur partagera le pays que tu verras.
29 Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.
Nous demeurâmes donc dans la vallée vis-à-vis de Beth-Pehor.