< Maimaitawar Shari’a 3 >

1 Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
Alors nous nous tournâmes, et nous montâmes par le chemin de Basan, et Hog le Roi de Basan sortit contre nous, avec tout son peuple pour combattre à Edréhi.
2 Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
Et l'Eternel me dit: Ne le crains point, car je l'ai livré entre tes mains, lui et tout son peuple, et son pays, et tu lui feras comme tu as fait a Sihon, Roi des Amorrhéens qui demeurait à Hesbon.
3 Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
Ainsi l'Eternel notre Dieu livra aussi entre nos mains Hog le Roi de Basan, et tout son peuple, et nous le battîmes tellement que nous ne lui laissâmes personne de reste.
4 A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
En ce même temps nous prîmes aussi toutes ses villes; [et] il n'y eut point de villes que nous ne lui prissions, [savoir] soixante villes, tout le pays d'Argob du royaume de Hog en Basan.
5 Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
Toutes ces villes-là étaient closes de hautes murailles, de portes et de barres, et outre cela il y avait des villes non murées en fort grand nombre.
6 Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
Et nous les détruisîmes à la façon de l'interdit, comme nous avions fait à Sihon, Roi de Hesbon, détruisant à la façon de l'interdit, toutes les villes, les hommes, les femmes, et les petits enfants.
7 Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
Mais nous pillâmes pour nous toutes les bêtes, et le butin des villes.
8 A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
Nous prîmes donc en ce temps-là le pays des deux Rois des Amorrhéens, qui étaient au deçà du Jourdain, depuis le torrent d'Arnon jusqu'à la montagne de Hermon.
9 (Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
[Or] les Sidoniens appellent Hermon, Sirjon; mais les Amorrhéens le nomment Sénir.
10 Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
Toutes les villes du plat pays et tout Galaad, et tout Basan jusqu'à Salca et Edréhi, les villes du Royaume de Hog en Basan.
11 (Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
Car Hog Roi de Basan était demeuré seul de reste des Réphaïms. Voici, son lit, qui est un lit de fer, n'est-il pas dans Rabba des enfants de Hammon? sa longueur est de neuf coudées, et sa largeur de quatre coudées, de coudée d'homme.
12 Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
En ce temps-là donc nous possédâmes ce pays-là; [et] je donnai aux Rubénites et aux Gadites ce qui est depuis Haroher, qui est sur le torrent d'Arnon, et la moitié de la montagne de Galaad, avec ses villes.
13 Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
Et je donnai à la demi-Tribu de Manassé le reste de Galaad, et tout Basan, qui était le Royaume de Hog; toute la contrée d'Argob par tout Basan, était appelée le pays des Réphaïms.
14 Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
Jaïr fils de Manassé prit toute la contrée d'Argob, jusqu'à la frontière des Guésuriens et des Mahacathiens, et il appela de son Nom ce pays de Basan, bourgs de Jaïr, lequel ils ont eu jusqu'à aujourd'hui.
15 Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
Je donnai aussi Galaad à Makir.
16 Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
Mais je donnai aux Rubénites et aux Gadites, depuis Galaad jusqu'au torrent d'Arnon, ce qui est enfermé par le torrent, et ses limites jusqu'au torrent de Jabbok, qui est la frontière des enfants de Hammon;
17 Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
Et la campagne, et le Jourdain, et [ses] confins depuis Kinnéreth jusqu'à la mer de la campagne, qui est la mer salée, au dessous d'Asdoth de Pisgar vers l'Orient.
18 Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
Or en ce temps-là je vous commandai, en disant: L'Eternel votre Dieu vous a donné ce pays pour le posséder, vous tous qui êtes vaillants, passez tous armés devant vos frères les enfants d'Israël.
19 Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
Que seulement vos femmes, vos petits enfants, et votre bétail, [car] je sais que vous avez beaucoup de bétail, demeurent dans les villes que je vous ai données.
20 sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
Jusqu'à ce que l'Eternel ait donné du repos à vos frères comme à vous, et qu'eux aussi possèdent le pays que l'Eternel votre Dieu leur va donner au delà du Jourdain; puis vous retournerez chacun en sa possession, laquelle je vous ai donnée.
21 A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
En ce temps-là aussi je commandai à Josué, en disant: Tes yeux ont vu tout ce que l'Eternel votre Dieu a fait à ces deux Rois; l'Eternel en fera de même à tous les Royaumes vers lesquels tu vas passer.
22 Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
Ne les craignez point; car l'Eternel votre Dieu combat lui-même pour vous.
23 A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
En ce même temps aussi je demandai grâce à l'Eternel, en disant:
24 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
Seigneur Eternel, tu as commencé de montrer à ton serviteur ta grandeur et ta main forte; car qui est le [Dieu] Fort au ciel et sur la terre qui puisse faire des œuvres comme les tiennes, et [dont la force soit] comme tes forces?
25 Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
Que je passe, je te prie, et que je voie le bon pays qui est au delà du Jourdain, cette bonne montagne, c'est à savoir, le Liban.
26 Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
Mais l'Eternel était fort irrité contre moi à cause de vous, et ne m'exauça point; mais il me dit: C'est assez, ne me parle plus de cette affaire.
27 Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
Monte au sommet de cette colline, et élève tes yeux vers l'Occident, et le Septentrion, vers le Midi, et l'Orient, et regarde de tes yeux; car tu ne passeras point ce Jourdain.
28 Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
Mais donnes-en la charge à Josué, et le fortifie, et le renforce; car c'est lui qui passera devant ce peuple, et qui les mettra en possession du pays que tu auras vu.
29 Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.
Ainsi nous sommes demeurés en cette vallée vis à viss de Beth-Péhor.

< Maimaitawar Shari’a 3 >