< Maimaitawar Shari’a 3 >

1 Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
Puis nous nous tournâmes, et nous montâmes par le chemin de Basan. Og, roi de Basan, sortit contre nous, lui et tout son peuple, pour nous combattre à Édréi.
2 Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
Yahvé me dit: « Ne le crains pas, car je l'ai livré entre tes mains, avec tout son peuple et son pays. Tu lui feras ce que tu as fait à Sihon, roi des Amoréens, qui habitait à Heshbon. »
3 Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
Et Yahvé, notre Dieu, livra aussi entre nos mains Og, roi de Basan, et tout son peuple. Nous le frappâmes jusqu'à ce qu'il ne lui restât plus personne.
4 A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
Nous avons pris toutes ses villes à cette époque. Il n'y eut pas une ville que nous n'ayons prise: soixante villes, toute la région d'Argob, le royaume d'Og en Basan.
5 Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
Toutes ces villes étaient fortifiées par de hautes murailles, des portes et des barres, sans compter les nombreux villages sans murailles.
6 Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
Nous les détruisîmes par interdit, comme nous l'avions fait à Sihon, roi de Heshbon, en dévastant par interdit toutes les villes habitées, avec les femmes et les petits enfants.
7 Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
Mais nous prîmes pour nous tout le bétail et le butin des villes.
8 A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
En ce temps-là, nous prîmes le pays de la main des deux rois des Amoréens qui étaient au-delà du Jourdain, depuis le val de l'Arnon jusqu'au mont Hermon.
9 (Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
(Les Sidoniens appellent Hermon Sirion, et les Amoréens l'appellent Senir.)
10 Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
Nous prîmes toutes les villes de la plaine, tout Galaad et tout Basan, jusqu'à Salca et Édréi, villes du royaume d'Og en Basan.
11 (Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
(Car il ne restait qu'Og, roi de Basan, du reste des Rephaïm. Voici, son sommier était un sommier de fer. N'est-ce pas à Rabba, chez les enfants d'Ammon? Sa longueur était de neuf coudées, et sa largeur de quatre coudées, selon la coudée d'un homme).
12 Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
En ce temps-là, nous prîmes possession de ce pays: depuis Arœr, qui est près du torrent de l'Arnon, et la moitié de la montagne de Galaad, avec ses villes, je les donnai aux Rubénites et aux Gadites;
13 Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
et le reste de Galaad, et tout Basan, le royaume d'Og, je les donnai à la demi-tribu de Manassé, toute la région d'Argob, tout Basan. (On appelle ce territoire le pays des Rephaïm.
14 Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
Jaïr, fils de Manassé, prit toute la région d'Argob, jusqu'à la frontière des Gueschuriens et des Maacathiens, et il leur donna le nom de Basan, d'après son propre nom, Havvoth Jaïr, jusqu'à ce jour).
15 Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
Je donnai Galaad à Makir.
16 Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
Je donnai aux Rubénites et aux Gadites, depuis Galaad jusqu'au torrent de l'Arnon, le milieu du torrent, et sa limite, jusqu'au fleuve Jabbok, qui est la limite des fils d'Ammon.
17 Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
La plaine, le Jourdain et sa limite, depuis Kinnéreth jusqu'à la mer de la plaine, la mer Salée, sous les pentes du Pisga, à l'orient.
18 Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
En ce temps-là, je vous ai donné cet ordre: « Yahvé ton Dieu t'a donné ce pays pour que tu en prennes possession. Vous tous, hommes de valeur, vous passerez armés devant vos frères, les enfants d'Israël.
19 Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
Mais vos femmes, vos petits enfants et vos troupeaux (je sais que vous avez beaucoup de bétail) habiteront dans les villes que je vous ai données,
20 sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
jusqu'à ce que l'Éternel donne du repos à vos frères, comme à vous, et qu'ils possèdent aussi le pays que l'Éternel, votre Dieu, leur donne au-delà du Jourdain. Alors vous retournerez chacun dans sa propriété, que je vous ai donnée. »
21 A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
En ce temps-là, je donnai cet ordre à Josué: « Tes yeux ont vu tout ce que Yahvé ton Dieu a fait à ces deux rois. C'est ainsi que Yahvé fera à tous les royaumes où tu passeras.
22 Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
Tu ne les craindras pas, car Yahvé ton Dieu combat lui-même pour toi. »
23 A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
En ce temps-là, je suppliai Yahvé, en disant:
24 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
« Seigneur Yahvé, tu as commencé à montrer à ton serviteur ta grandeur et ta main puissante. Car quel dieu y a-t-il dans les cieux et sur la terre qui puisse faire des œuvres comme les tiennes, et des actes de puissance comme les tiens?
25 Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
Je t'en prie, laisse-moi aller voir le bon pays qui est au-delà du Jourdain, cette belle montagne et le Liban. »
26 Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
Mais Yahvé s'est mis en colère contre moi à cause de vous, et il ne m'a pas écouté. L'Éternel m'a dit: « C'est assez! Ne me parle plus de cette affaire.
27 Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
Monte au sommet du Pisga, et lève tes yeux vers l'ouest, le nord, le sud et l'est, et regarde de tes yeux, car tu ne passeras pas ce Jourdain.
28 Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
Mais commandez à Josué, encouragez-le et fortifiez-le, car il passera devant ce peuple, et il lui fera hériter le pays que vous verrez. »
29 Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.
Nous restâmes donc dans la vallée, près de Beth Peor.

< Maimaitawar Shari’a 3 >