< Maimaitawar Shari’a 3 >

1 Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
And so we turneden, and stieden bi the weie of Basan; and Og, the kyng of Basan, yede out ayens vs with his puple, to fiyte in Edrai.
2 Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
And the Lord seide to me, Drede thou not hym, for he is bitakun in thin hond, with al his puple, and his lond; and thou schalt do to hym, as thou didist to Seon, kyng of Ammoreis, that dwellide in Esebon.
3 Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
Therfor oure Lord God bitook in oure hondis also Og, kyng of Basan, and al his puple; and we han smyte hym `til to deeth,
4 A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
and wastiden alle the citees `of him in o tyme; no town was that ascapide vs; `we destrieden sixti citees, al the cuntrei of Argob, of the rewme of Og in Basan.
5 Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
Alle the citees weren strengthid with hiyest wallis, and with yatis and barris; with out townes vnnoumbrable, that hadden not wallis.
6 Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
And we diden awey thilke men, as we diden to Seon, kyng of Esebon; and we losten ech citee, and men, and wymmen, and litle children;
7 Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
forsothe we token bi prey beestis, and the spuylis of citees.
8 A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
And we token in that tyme the lond fro the hond of twey kyngis of Ammorreis, that weren biyonde Jordan, fro the stronde of Arnon `til to the hil of Hermon,
9 (Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
`which hil Sidonyes clepen Sarion, and Ammorreis clepen Sanyr.
10 Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
We tooken alle the citees that weren set in the pleyn, and al the lond of Galaad, and of Basan, `til to Selcha and Edray, citees of the rewme of Og, in Basan.
11 (Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
For Og aloone, kyng of Basan, was left of the generacioun of giauntis; and his yrun bed is schewid, which is in Rabath, of the sones of Amon, and hath nyne cubitis of lengthe, and foure cubitis of breede, at the mesure of a cubit of mannus hond.
12 Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
And we weldiden in that tyme the lond, fro Aroer, which is on the `brynke of the stronde of Arnon, `til to the myddil paart of the hil of Galaad; and Y yaf the citees `of hym to Ruben and Gad.
13 Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
Forsothe Y yaf the tother part of Galaad, and al Basan, of the rewme of Og, to the half lynage of Manasses, and al the cuntrei of Argob. Al Basan was clepid the lond of giauntis.
14 Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
Jair, `sone of Manasses, weldide al the cuntrey of Argob, `til to the lond of Gesuri and of Machati; and he clepide bi his name Basan Anothiair, that is, the townes of Jair, til in to present dai.
15 Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
Also Y yaf Galaad to Machir; and to the lynagis of Ruben and of Gad Y yaf the lond of Galaad, `til to the strond of Arnon, the myddil of the stronde,
16 Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
and of the endis `til to the stronde of Jeboth, which is the terme of `the sones of Amon.
17 Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
And Y yaf the pleyn of the wildernesse `til to Jordan, and the termes of Cenereth `til to the see of deseert, which see is moost salt, at the rotis of the hil of Phasga, ayens the eest.
18 Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
And Y comaundide to you in that tyme, and seide, Youre Lord God yyueth to you this lond in to erytage;
19 Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
alle ye stronge men, without wyues and litle children and beestis, be maad redi, and `go ye bifor youre brithren, the sones of Israel. For Y knowe that ye han many beestis, and tho schulen dwelle in citees whiche Y yaf to you,
20 sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
til the Lord yyue reste to youre brithren, as he yaf to you, and til thei also welden the lond `which the Lord schal yyue to hem biyonde Jordan; thanne ech man schal turne ayen in to his possessioun which Y yaf to you.
21 A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
Also Y comaundid to Josue in that tyme, and seide, Thin iyen sien what thingis youre Lord God dide to these twei kyngis; so he schal do to alle rewmes, to whiche thou schalt go; drede thou not hem.
22 Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
And Y preiede the Lord in that tyme,
23 A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
and seide, Lord God, thou hast bigunne to schewe to thi seruaunt thi greetnesse, and strongeste hond,
24 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
for noon other God is ether in heuene, ether in erthe, that mai do thi werkis, and may be comparisound to thi strengthe.
25 Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
Therfor Y schal passe, and schal se this beeste lond biyende Jordan, and this noble hil and Liban.
26 Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
And the Lord was wrooth to me for you, nethir he herde me, but seide to me, It suffisith to thee; speke thou no more of this thing to me.
27 Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
`Stye thou in to the hiynesse of Phasga, and caste aboute thin iyen to the west, and north, and south, and eest, and biholde, for thou schalt not passe this Jordan.
28 Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
Comaunde thou to Josue, and strengthe thou and coumforte hym; for he schal go bifore this puple, and he schal departe to hem the lond, which thou schalt se.
29 Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.
And we dwelliden in the valey ayens the temple of Phegor.

< Maimaitawar Shari’a 3 >