< Maimaitawar Shari’a 3 >

1 Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
Then we turned, and went up the way to Bashan; and Og the king of Bashan came out against us, he and all his people, unto battle at Edrei.
2 Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
And the LORD said unto me: 'Fear him not; for I have delivered him, and all his people, and his land, into thy hand; and thou shalt do unto him as thou didst unto Sihon king of the Amorites, who dwelt at Heshbon.'
3 Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
So the LORD our God delivered into our hand Og also, the king of Bashan, and all his people; and we smote him until none was left to him remaining.
4 A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
And we took all his cities at that time; there was not a city which we took not from them; threescore cities, all the region of Argob, the kingdom of Og in Bashan.
5 Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
All these were fortified cities, with high walls, gates, and bars; beside the unwalled towns a great many.
6 Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
And we utterly destroyed them, as we did unto Sihon king of Heshbon, utterly destroying every city, the men, and the women, and the little ones.
7 Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
But all the cattle, and the spoil of the cities, we took for a prey unto ourselves.
8 A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
And we took the land at that time out of the hand of the two kings of the Amorites that were beyond the Jordan, from the valley of Arnon unto mount Hermon —
9 (Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
which Hermon the Sidonians call Sirion, and the Amorites call it Senir —
10 Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
all the cities of the plain, and all Gilead, and all Bashan, unto Salcah and Edrei, cities of the kingdom of Og in Bashan. —
11 (Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
For only Og king of Bashan remained of the remnant of the Rephaim; behold, his bedstead was a bedstead of iron; is it not in Rabbah of the children of Ammon? nine cubits was the length thereof, and four cubits the breadth of it, after the cubit of a man. —
12 Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
And this land we took in possession at that time; from Aroer, which is by the valley of Arnon, and half the hill-country of Gilead, and the cities thereof, gave I unto the Reubenites and to the Gadites;
13 Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
and the rest of Gilead, and all Bashan, the kingdom of Og, gave I unto the half-tribe of Manasseh; all the region of Argob — all that Bashan is called the land of Rephaim.
14 Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
Jair the son of Manasseh took all the region of Argob, unto the border of the Geshurites and the Maacathites, and called them, even Bashan, after his own name, Havvoth-jair, unto this day. —
15 Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
And I gave Gilead unto Machir.
16 Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
And unto the Reubenites and unto the Gadites I gave from Gilead even unto the valley of Arnon, the middle of the valley for a border; even unto the river Jabbok, which is the border of the children of Ammon;
17 Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
the Arabah also, the Jordan being the border thereof, from Chinnereth even unto the sea of the Arabah, the Salt Sea, under the slopes of Pisgah eastward.
18 Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
And I commanded you at that time, saying: 'The LORD your God hath given you this land to possess it; ye shall pass over armed before your brethren the children of Israel, all the men of valour.
19 Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
But your wives, and your little ones, and your cattle — I know that ye have much cattle — shall abide in your cities which I have given you;
20 sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
until the LORD give rest unto your brethren, as unto you, and they also possess the land which the LORD your God giveth them beyond the Jordan; then shall ye return every man unto his possession, which I have given you.
21 A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
And I commanded Joshua at that time, saying: 'Thine eyes have seen all that the LORD your God hath done unto these two kings; so shall the LORD do unto all the kingdoms whither thou goest over.
22 Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
Ye shall not fear them; for the LORD your God, He it is that fighteth for you.'
23 A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
And I besought the LORD at that time, saying:
24 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
'O Lord GOD, Thou hast begun to show Thy servant Thy greatness, and Thy strong hand; for what god is there in heaven or on earth, that can do according to Thy works, and according to Thy mighty acts?
25 Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
Let me go over, I pray Thee, and see the good land that is beyond the Jordan, that goodly hill-country, and Lebanon.'
26 Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
But the LORD was wroth with me for your sakes, and hearkened not unto me; and the LORD said unto me: 'Let it suffice thee; speak no more unto Me of this matter.
27 Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
Get thee up into the top of Pisgah, and lift up thine eyes westward, and northward, and southward, and eastward, and behold with thine eyes; for thou shalt not go over this Jordan.
28 Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
But charge Joshua, and encourage him, and strengthen him; for he shall go over before this people, and he shall cause them to inherit the land which thou shalt see.'
29 Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.
So we abode in the valley over against Beth-peor.

< Maimaitawar Shari’a 3 >