< Maimaitawar Shari’a 3 >

1 Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
We set off and went up the road towards Bashan. Og, king of Bashan, and his whole army came out to fight us at Edrei.
2 Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
But the Lord told me, “Don't be afraid of him, for I have handed him over to you, together with all his people and his land. Deal with him as you did with Sihon, king of the Amorites, who ruled in Heshbon.”
3 Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
So the Lord our God handed over to us Og, king of Bashan, and his whole army as well. We killed them and left no survivors.
4 A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
We also captured all his towns. There wasn't a single town among all the sixty that we didn't capture. This included the whole region of Argob, the kingdom of Og in Bashan.
5 Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
All of these towns were fortified with high walls and gates with bars. There were many more villages as well, those that didn't have walls.
6 Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
We set them apart for destruction, just as we did to Sihon, king of Heshbon, killing all the men, women, and children of every city.
7 Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
But we took for ourselves all the livestock and plunder from the towns.
8 A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
So in summary, at that time we took from the two Amorite kings the land east of the Jordan, from the Arnon Valley all the way to Mount Hermon.
9 (Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
(Mount Hermon is called Sirion by the Sidonians and Senir by the Amorites.)
10 Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
The area included all the towns of the plain, all of Gilead, and all of Bashan, up to and including the towns of Salecah and Edrei in the kingdom of Og.
11 (Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
(Only Og, king of Bashan, was left of the race of the Rephaim. He had a bed made of iron that was nine cubits long and four cubits wide. It's still in the Ammonite town of Rabbah.)
12 Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
This is when we took over the land. I assigned to the tribes of Reuben and Gad the land to the north of the town of Aroer in the Arnon Valley, and half the hill country of Gilead, together with its towns.
13 Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
I assigned to the half-tribe of Manasseh the rest of Gilead, and all of Bashan, the kingdom of Og. (The whole region of Argob, all the territory of Bashan, was formerly called the land of the Rephaim.)
14 Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
Jair, a descendant of Manasseh, took over the whole region of Argob right up to the border of the Geshurites and Maacathites and changed the name of Bashan to Havvoth-jair after himself, which is still its name to this day.
15 Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
I assigned the rest of Gilead to the descendants of Machir,
16 Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
while I assigned to the tribes of Reuben and Gad the area from Gilead to the Arnon Valley, the boundary line being the middle of the valley, all the way to the Jabbok River on the Ammonite border.
17 Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
The Jordan River in the Arabah bordered it to the west, from the Sea of Galilee to the Sea of the Arabah (the Dead Sea). On the east lay the slopes of the Pisgah mountain range.
18 Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
This was when I gave you these instructions: “The Lord your God has given you this country as yours to own. All your warriors are to cross over, ready for battle, leading your fellow Israelites.
19 Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
However, your wives, your children, and your livestock (I know that you have plenty of livestock) can stay behind in the towns I have given you,
20 sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
until the Lord gives victory to your fellow Israelites and they have peace, just as he has for you, after taking over the land that the Lord your God is giving them on the other side of the Jordan. Then you can all return to the land I have given you to own.”
21 A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
This was the time I ordered Joshua: “You've seen with your own eyes seen everything the Lord your God did to these two kings. The Lord will do the same to all the kingdoms where you're going.
22 Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
Don't be afraid of them, for the Lord your God himself will be fighting on your side.”
23 A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
This was also the time I pleaded with the Lord, saying,
24 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
“Lord God, you've really only just begun to show your power and greatness to me, your servant. What god in heaven or on earth has the incredible ability to do the mighty acts you do?
25 Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
Please, let me cross over the Jordan and see the good land there, the beautiful hills, and the mountains of Lebanon!”
26 Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
But the Lord was angry with me because of you, and he refused to listen to me. “That's enough,” he told me. “Don't talk to me about this anymore.
27 Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
Climb up to the top of Mount and look west, north, south, and east. Take a long look at the land with your own eyes, because you're not going to cross this Jordan.
28 Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
Instead, put Joshua in charge because he's the one who will cross over, leading the people and helping them to take over the land that you see. Encourage him and support him.”
29 Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.
So we remained there in the valley near Beth-peor.

< Maimaitawar Shari’a 3 >