< Maimaitawar Shari’a 29 >
1 Waɗannan su ne sharuɗan alkawarin da Ubangiji ya umarci Musa yă yi da Isra’ilawa a Mowab, wato, ban da alkawarin da ya yi da su a Dutsen Horeb.
Estas são as palavras do concerto que o Senhor ordenou a Moysés na terra de Moab, que fizesse com os filhos de Israel, além do concerto que fizera com elles em Horeb.
2 Sai Musa ya tara dukan Isra’ila, ya ce musu, Idanunku sun ga dukan abin da Ubangiji ya yi a Masar ga Fir’auna, ga kuma dukan shugabanninsa da kuma ga dukan ƙasarsa.
E chamou Moysés a todo o Israel, e disse-lhes: Tendes visto tudo quanto o Senhor fez na terra do Egypto, perante vossos olhos, a Pharaó, e a todos os seus servos, e a toda a sua terra:
3 Da idanunku kun ga waɗannan gwaje-gwaje, waɗannan alamu masu banmamaki, da al’ajabai masu girma.
As grandes provas que os teus olhos teem visto, aquelles signaes e grandes maravilhas:
4 Duk da haka har wa yau Ubangiji bai ba ku hankalin ganewa, ko idanun da za su gani, ko kunnuwan da za su ji ba.
Porém não vos tem dado o Senhor um coração para entender, nem olhos para ver, nem ouvidos para ouvir, até ao dia de hoje
5 Shekaru arba’in da na jagorance ku cikin hamada, tufafinku ba su yage ba, haka kuwa takalman da suke a ƙafafunku.
E quarenta annos vos fiz andar pelo deserto: não se envelheceram sobre vós os vossos vestidos, e nem se envelheceu no teu pé o teu sapato.
6 Ba ku ci burodi ba, ba ku kuwa sha ruwan inabi, ko wani abu mai sa jiri ba. Ya yi haka don ku san cewa shi ne Ubangiji Allahnku.
Pão não comestes, e vinho e bebida forte não bebestes: para que soubesseis que eu sou o Senhor vosso Deus.
7 Sa’ad da kuka kai wannan wuri, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan, suka fito don su yi yaƙi da mu, amma muka ci su da yaƙi.
Vindo vós pois a este logar, Sehon, rei de Hesbon, e Og, rei de Basan, nos sairam ao encontro, á peleja, e nós os ferimos:
8 Muka ƙwace ƙasarsu, muka ba da ita gādo ga mutanen Ruben, mutanen Gad, da kuma rabin mutanen Manasse.
E tomámos a sua terra, e a démos por herança aos rubenitas, e aos gaditas, e á meia tribu dos manassitas.
9 Saboda haka sai ku kiyaye, ku bi sharuɗan wannan alkawari, don ku yi nasara a cikin kome da kuke yi.
Guardae pois as palavras d'este concerto, e fazei-as, para que prospereis em tudo quanto fizerdes.
10 Yau, ga ku nan tsaye, dukanku a gaban Ubangiji Allahnku, shugabanninku da manyan mutanenku, dattawanku da hafsoshinku, da kuma dukan sauran mutanen Isra’ila,
Vós todos estaes hoje perante o Senhor vosso Deus: os Cabeças de vossas tribus, vossos anciãos, e os vossos officiaes, todo o homem de Israel;
11 tare da’ya’yanku da matanku, da baƙin da suke zama sansanoninku, har ma da waɗanda suke muku faskare, da waɗanda suke ɗiba muku ruwa.
Os vossos meninos, as vossas mulheres, e o estrangeiro que está no meio do teu arraial; desde o rachador da tua lenha até ao tirador da tua agua;
12 Kuna tsaye a nan don ku yi alkawari da Ubangiji Allahnku, alkawarin da Ubangiji yake yi ta wurin rantsuwa da ku a wannan rana,
Para que entres no concerto do Senhor teu Deus, e no seu juramento que o Senhor teu Deus hoje faz comtigo;
13 don yă mai da ku jama’arsa yau, shi kuwa yă zama Allahnku kamar yadda ya yi muku alkawari, da yadda kuma ya rantse wa kakanninku, Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.
Para que hoje te confirme a si por povo, e elle te seja a ti por Deus, como te tem dito, e como jurou a teus paes, Abrahão, Isaac e Jacob.
14 Ina yin wannan alkawari da rantsuwar, ba da ku kaɗai da
E não sómente comvosco faço este concerto e este juramento,
15 kuke tsattsaye a nan tare da mu a yau a gaban Ubangiji Allahnmu ba, amma har da waɗanda ba sa nan yau.
Mas com aquelle que hoje está aqui em pé comnosco perante o Senhor nosso Deus, e com aquelle que hoje não está aqui comnosco.
16 Ku kanku kun san yadda muka yi zama a Masar, da yadda muka yi ta ratsawa ta tsakiyar al’ummai muka wuce.
Porque vós sabeis como habitámos na terra do Egypto, e como passámos pelo meio das nações pelas quaes passastes;
17 A cikinsu, kun ga siffofi masu banƙyama da gumaka na itace da dutse, na azurfa da zinariya.
E vistes as suas abominações, e os seus idolos, o pau e a pedra, a prata e o oiro que havia entre elles.
18 Kada zuciyar wani mutum, ko ta wata mata ko na wani iyali, ko wata kabila cikinku yau, ta bar bin Ubangiji Allahnku, tă koma ga bauta wa gumakan waɗannan al’ummai. Kada a sami wani tushe mai ba da’ya’ya masu dafi, masu ɗaci a cikinku.
Para que entre vós não haja homem, nem mulher, nem familia, nem tribu, cujo coração hoje se desvie do Senhor nosso Deus, para que vá servir aos deuses d'estas nações; para que entre vós não haja raiz que dê fel e absintho;
19 Idan kuma wani mutum ya ji kalmomi na wannan rantsuwa, ya kuma sa wa kansa albarka yana tunani cewa, “Ba abin da zai same ni, ko da na nace a taurinkaina.” Wannan zai jawo lalacewar dukan Isra’ila tare da kai.
E aconteça que, ouvindo as palavras d'esta maldição, se abençôe no seu coração, dizendo: Terei paz, ainda que ande conforme ao bom parecer do meu coração; para accrescentar á sêde a bebedice
20 Ubangiji ba zai gafarce shi ba, fushinsa da kishinsa za su ƙuna a kan wannan mutum. Dukan la’anonin da aka rubuta a wannan littafi za su fāɗo a kansa, Ubangiji kuwa zai shafe sunansa daga ƙarƙashin sama.
O Senhor não lhe quererá perdoar; mas então fumegará a ira do Senhor e o seu zelo sobre o tal homem, e toda a maldição escripta n'este livro jazerá sobre elle; e o Senhor apagará o seu nome de debaixo do céu.
21 Ubangiji zai ware shi daga dukan kabilan Isra’ila don yă hukunta shi bisa ga dukan la’anonin alkawarin da aka rubuta a wannan Littafin Doka.
E o Senhor o separará para mal de todas as tribus de Israel, conforme a todas as maldições do concerto escripto no livro d'esta lei.
22 Tsararraki masu zuwa nan gaba, wato,’ya’yan da za su gāje ku, da baƙon da ya zo daga ƙasa mai nisa, za su ga annobar ƙasar, da cuce-cucen da Ubangiji ya buge ta da su.
Então dirá a geração vindoura, os vossos filhos, que se levantarem depois de vós, e o estranho que virá de terras remotas, vendo as pragas d'esta terra, e as suas doenças, com que o Senhor a terá affligido;
23 Ƙasar gaba ɗaya za tă zama gishiri mai ƙuna marar amfani da kuma kibiritu, babu shuki, babu abin da yake tsirowa, babu itatuwan da suke girma a cikinta. Za tă zama kamar yadda aka hallaka Sodom da Gomorra, Adma da Zeboyim, waɗanda Ubangiji ya hallaka cikin zafin fushinsa.
E toda a sua terra abrazada com enxofre e sal, de sorte que não será semeada, e nada produzirá, nem n'ella crescerá herva alguma: assim como foi a destruição de Sodoma e de Gomorrha, de Adama e de Zeboim, que o Senhor destruiu na sua ira e no seu furor
24 Dukan al’ummai za su yi tambaya su ce, “Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan ƙasa? Me ya jawo wannan fushi mai tsanani haka?”
E todas as nações dirão: Porque fez o Senhor assim com esta terra? qual foi a causa do furor d'esta tão grande ira
25 Amsar kuwa za tă zama, “Wannan ya zama haka domin wannan mutane, sun yi watsi da alkawarin Ubangiji Allah na kakanninsu, alkawarin da ya yi da su sa’ad da ya fitar da su daga Masar.
Então se dirá: Porquanto deixaram o concerto do Senhor, o Deus de seus paes, que com elles tinha feito, quando os tirou do Egypto.
26 Sun juya, suka bauta wa waɗansu alloli, suka rusuna musu, allolin da ba su sani ba, allolin da Ubangiji bai ba su ba.
E elles foram-se, e serviram a outros deuses, e se inclinaram diante d'elles; deuses que os não conheceram, e nenhum dos quaes elle lhes tinha dado.
27 Saboda haka fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan wannan ƙasa, har ya kawo dukan la’anoni da aka rubuta a wannan littafi a kanta.
Pelo que a ira do Senhor se accendeu contra esta terra, para trazer sobre ella toda a maldição que está escripta n'este livro.
28 Cikin zafin fushi da babbar hasala Ubangiji ya tumɓuke su daga ƙasarsu, ya watsar da su cikin wata ƙasa dabam, kamar yadda suke a yau.”
E o Senhor os tirou da sua terra com ira, e com indignação, e com grande furor, e os lançou em outra terra, como n'este dia se vê
29 Ubangiji Allahnmu bai bayyana abubuwa na yanzu da na nan gaba ba, amma ya umarce mu mu kiyaye kalmomin dokar da ya ba mu, mu da kuma’ya’yanmu har abada.
As coisas encobertas são para o Senhor nosso Deus; porém as reveladas são para nós e para nossos filhos para sempre, para fazer todas as palavras d'esta lei