< Maimaitawar Shari’a 29 >

1 Waɗannan su ne sharuɗan alkawarin da Ubangiji ya umarci Musa yă yi da Isra’ilawa a Mowab, wato, ban da alkawarin da ya yi da su a Dutsen Horeb.
La ngamazwi esivumelwano iNkosi eyamlaya uMozisi ukusenza labantwana bakoIsrayeli elizweni lakoMowabi, ngaphandle kwesivumelwano eyayisenze labo eHorebe.
2 Sai Musa ya tara dukan Isra’ila, ya ce musu, Idanunku sun ga dukan abin da Ubangiji ya yi a Masar ga Fir’auna, ga kuma dukan shugabanninsa da kuma ga dukan ƙasarsa.
UMozisi wasebiza uIsrayeli wonke, wathi kubo: Lina libonile konke iNkosi eyakwenza phambi kwamehlo enu elizweni leGibhithe, kuFaro lakuzo zonke inceku zakhe lakulo lonke ilizwe lakhe,
3 Da idanunku kun ga waɗannan gwaje-gwaje, waɗannan alamu masu banmamaki, da al’ajabai masu girma.
izilingo ezinkulu amehlo akho azibonileyo, izibonakaliso lalezozimangaliso ezinkulu.
4 Duk da haka har wa yau Ubangiji bai ba ku hankalin ganewa, ko idanun da za su gani, ko kunnuwan da za su ji ba.
Kodwa iNkosi kayilinikanga inhliziyo yokuqedisisa lamehlo okubona lendlebe zokuzwa kuze kube lamuhla.
5 Shekaru arba’in da na jagorance ku cikin hamada, tufafinku ba su yage ba, haka kuwa takalman da suke a ƙafafunku.
Ngilihambise iminyaka engamatshumi amane enkangala. Izembatho zenu kaziguganga phezu kwenu, lenyathela lakho kaliguganga enyaweni lwakho;
6 Ba ku ci burodi ba, ba ku kuwa sha ruwan inabi, ko wani abu mai sa jiri ba. Ya yi haka don ku san cewa shi ne Ubangiji Allahnku.
kalidlanga sinkwa, kalinathanga iwayini lokunathwayo okulamandla, ukuze lazi ukuthi ngiyiNkosi uNkulunkulu wenu.
7 Sa’ad da kuka kai wannan wuri, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan, suka fito don su yi yaƙi da mu, amma muka ci su da yaƙi.
Ekufikeni kwenu kulindawo, uSihoni inkosi yeHeshiboni loOgi inkosi yeBashani baphuma ukumelana lathi empini, kodwa sabatshaya,
8 Muka ƙwace ƙasarsu, muka ba da ita gādo ga mutanen Ruben, mutanen Gad, da kuma rabin mutanen Manasse.
sathatha ilizwe labo, salinika laba yilifa kwabakoRubeni lakwabakoGadi lakungxenye yesizwe sakoManase.
9 Saboda haka sai ku kiyaye, ku bi sharuɗan wannan alkawari, don ku yi nasara a cikin kome da kuke yi.
Ngakho gcinani amazwi alesisivumelwano liwenze, ukuze liphumelele kukho konke elikwenzayo.
10 Yau, ga ku nan tsaye, dukanku a gaban Ubangiji Allahnku, shugabanninku da manyan mutanenku, dattawanku da hafsoshinku, da kuma dukan sauran mutanen Isra’ila,
Lina lonke limi phambi kweNkosi uNkulunkulu wenu lamuhla, inhloko zenu, izizwe zenu, abadala benu, lezinduna zenu, wonke amadoda akoIsrayeli,
11 tare da’ya’yanku da matanku, da baƙin da suke zama sansanoninku, har ma da waɗanda suke muku faskare, da waɗanda suke ɗiba muku ruwa.
abantwanyana benu, omkenu, lowemzini ophakathi kwenkamba yakho, kusukela kumgamuli wenkuni zakho kuze kube kumukhi wamanzi akho,
12 Kuna tsaye a nan don ku yi alkawari da Ubangiji Allahnku, alkawarin da Ubangiji yake yi ta wurin rantsuwa da ku a wannan rana,
ukwedlulela esivumelwaneni seNkosi uNkulunkulu wakho lesifungweni sayo, iNkosi uNkulunkulu wakho esenza lawe lamuhla,
13 don yă mai da ku jama’arsa yau, shi kuwa yă zama Allahnku kamar yadda ya yi muku alkawari, da yadda kuma ya rantse wa kakanninku, Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.
ukuze ikumise lamuhla ube yisizwe sayo, lokuthi yona ibe nguNkulunkulu wakho, njengokutsho kwayo kuwe lanjengokufunga kwayo kuboyihlo, kuAbrahama, kuIsaka lakuJakobe.
14 Ina yin wannan alkawari da rantsuwar, ba da ku kaɗai da
Njalo kangisenzi lani lodwa lesisivumelwano lalesisifungo,
15 kuke tsattsaye a nan tare da mu a yau a gaban Ubangiji Allahnmu ba, amma har da waɗanda ba sa nan yau.
kodwa lalowo olapha lathi, omiyo lamuhla phambi kweNkosi uNkulunkulu wethu, njalo lalowo ongekho lapha lathi lamuhla.
16 Ku kanku kun san yadda muka yi zama a Masar, da yadda muka yi ta ratsawa ta tsakiyar al’ummai muka wuce.
Ngoba lina liyazi ukuthi sahlala njani elizweni leGibhithe, lokuthi sadabula njani phakathi kwezizwe eladabula kuzo;
17 A cikinsu, kun ga siffofi masu banƙyama da gumaka na itace da dutse, na azurfa da zinariya.
njalo libonile izinengiso zazo, lezithombe zazo, isigodo lelitshe, isiliva legolide, ezazilazo.
18 Kada zuciyar wani mutum, ko ta wata mata ko na wani iyali, ko wata kabila cikinku yau, ta bar bin Ubangiji Allahnku, tă koma ga bauta wa gumakan waɗannan al’ummai. Kada a sami wani tushe mai ba da’ya’ya masu dafi, masu ɗaci a cikinku.
Hlezi kube khona phakathi kwenu indoda kumbe owesifazana kumbe usapho kumbe isizwe, onhliziyo yakhe iphambuka lamuhla isuka eNkosini uNkulunkulu wethu ukuyakhonza onkulunkulu balezizizwe. Hlezi kube khona phakathi kwenu impande ethela izithelo ezilobuhlungu lezibabayo.
19 Idan kuma wani mutum ya ji kalmomi na wannan rantsuwa, ya kuma sa wa kansa albarka yana tunani cewa, “Ba abin da zai same ni, ko da na nace a taurinkaina.” Wannan zai jawo lalacewar dukan Isra’ila tare da kai.
Njalo kuzakuthi nxa esizwa amazwi alesisiqalekiso, azibusise enhliziyweni yakhe esithi: Ngizakuba lokuthula lanxa ngihamba ebuqholweni benhliziyo yami; ukuze kuqedwe okumanzi kanye lokomileyo.
20 Ubangiji ba zai gafarce shi ba, fushinsa da kishinsa za su ƙuna a kan wannan mutum. Dukan la’anonin da aka rubuta a wannan littafi za su fāɗo a kansa, Ubangiji kuwa zai shafe sunansa daga ƙarƙashin sama.
INkosi kayiyikuvuma ukumthethelela, kodwa khona intukuthelo yeNkosi lobukhwele bayo kuzathunqela leyondoda, njalo sonke isiqalekiso esibhaliweyo egwalweni lolu sizalala phezu kwayo, leNkosi icitshe ibizo layo lisuke ngaphansi kwamazulu.
21 Ubangiji zai ware shi daga dukan kabilan Isra’ila don yă hukunta shi bisa ga dukan la’anonin alkawarin da aka rubuta a wannan Littafin Doka.
LeNkosi izayehlukanisela ububi iyikhuphe kuzo zonke izizwe zakoIsrayeli, njengazo zonke iziqalekiso zesivumelwano ezibhaliweyo egwalweni lwalumlayo.
22 Tsararraki masu zuwa nan gaba, wato,’ya’yan da za su gāje ku, da baƙon da ya zo daga ƙasa mai nisa, za su ga annobar ƙasar, da cuce-cucen da Ubangiji ya buge ta da su.
Khona sizakuthi isizukulwana esizayo, abantwana benu, abazavela emva kwenu, lowezizwe ovela elizweni elikhatshana, lapho bebona inhlupheko zalelilizwe lezifo iNkosi eligulise ngazo,
23 Ƙasar gaba ɗaya za tă zama gishiri mai ƙuna marar amfani da kuma kibiritu, babu shuki, babu abin da yake tsirowa, babu itatuwan da suke girma a cikinta. Za tă zama kamar yadda aka hallaka Sodom da Gomorra, Adma da Zeboyim, waɗanda Ubangiji ya hallaka cikin zafin fushinsa.
ilizwe lonke lalo lizakuba yisibabule letshwayi lokutshiswa, alihlanyelwanga, kalimilisi, kakulalatshani obumila kulo, njengokubhujiswa kweSodoma leGomora, iAdima leZeboyimi, iNkosi eyayibhubhisa entukuthelweni yayo lelakeni lwayo,
24 Dukan al’ummai za su yi tambaya su ce, “Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan ƙasa? Me ya jawo wannan fushi mai tsanani haka?”
lazo zonke izizwe zizakuthi: Kungani iNkosi yenze kanje kulelilizwe? Kuyini ukuvutha kwalolulaka olukhulu?
25 Amsar kuwa za tă zama, “Wannan ya zama haka domin wannan mutane, sun yi watsi da alkawarin Ubangiji Allah na kakanninsu, alkawarin da ya yi da su sa’ad da ya fitar da su daga Masar.
Khona bazakuthi: Ngoba batshiyile isivumelwano seNkosi uNkulunkulu waboyise, eyasenza labo ekubakhupheni kwayo elizweni leGibhithe.
26 Sun juya, suka bauta wa waɗansu alloli, suka rusuna musu, allolin da ba su sani ba, allolin da Ubangiji bai ba su ba.
Bahamba bakhonza abanye onkulunkulu babakhothamela, onkulunkulu abangabaziyo, eyayingababelanga.
27 Saboda haka fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan wannan ƙasa, har ya kawo dukan la’anoni da aka rubuta a wannan littafi a kanta.
Lentukuthelo yeNkosi yalivuthela lelilizwe, ukwehlisela kulo zonke iziqalekiso ezibhaliweyo egwalweni lolu.
28 Cikin zafin fushi da babbar hasala Ubangiji ya tumɓuke su daga ƙasarsu, ya watsar da su cikin wata ƙasa dabam, kamar yadda suke a yau.”
Njalo iNkosi yabasiphuna elizweni labo ngentukuthelo langolaka langenzondo enkulu, yabaphosela kwelinye ilizwe njengalamuhla.
29 Ubangiji Allahnmu bai bayyana abubuwa na yanzu da na nan gaba ba, amma ya umarce mu mu kiyaye kalmomin dokar da ya ba mu, mu da kuma’ya’yanmu har abada.
Imfihlo ngezeNkosi uNkulunkulu wethu, kodwa izinto ezembuliweyo zingezethu lezabantwana bethu kuze kube nininini, ukwenza wonke amazwi alumlayo.

< Maimaitawar Shari’a 29 >