< Maimaitawar Shari’a 29 >

1 Waɗannan su ne sharuɗan alkawarin da Ubangiji ya umarci Musa yă yi da Isra’ilawa a Mowab, wato, ban da alkawarin da ya yi da su a Dutsen Horeb.
Ce sont ici les paroles de l'alliance que l'Eternel commanda à Moïse de traiter avec les enfants d'Israël, au pays de Moab, outre l'alliance qu'il avait traitée avec eux en Horeb.
2 Sai Musa ya tara dukan Isra’ila, ya ce musu, Idanunku sun ga dukan abin da Ubangiji ya yi a Masar ga Fir’auna, ga kuma dukan shugabanninsa da kuma ga dukan ƙasarsa.
Moïse donc appela tout Israël, et leur dit: Vous avez vu tout ce que l'Eternel a fait en votre présence dans le pays d'Egypte, à Pharaon et à tous ses serviteurs, et à tout son pays.
3 Da idanunku kun ga waɗannan gwaje-gwaje, waɗannan alamu masu banmamaki, da al’ajabai masu girma.
Les grandes épreuves que tes yeux ont vues, ces signes, et ces grands miracles.
4 Duk da haka har wa yau Ubangiji bai ba ku hankalin ganewa, ko idanun da za su gani, ko kunnuwan da za su ji ba.
Mais l'Eternel ne vous a point donné un cœur pour entendre, ni des yeux pour voir, ni des oreilles pour entendre, jusqu'à aujourd'hui.
5 Shekaru arba’in da na jagorance ku cikin hamada, tufafinku ba su yage ba, haka kuwa takalman da suke a ƙafafunku.
Et je vous ai conduits durant quarante ans par le désert, sans que vos vêtements se soient envieillis sur vous, et sans que ton soulier ait été envieilli sur ton pied.
6 Ba ku ci burodi ba, ba ku kuwa sha ruwan inabi, ko wani abu mai sa jiri ba. Ya yi haka don ku san cewa shi ne Ubangiji Allahnku.
Vous n'avez point mangé de pain, ni bu de vin, ni de cervoise, afin que vous connaissiez que je suis l'Eternel votre Dieu.
7 Sa’ad da kuka kai wannan wuri, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan, suka fito don su yi yaƙi da mu, amma muka ci su da yaƙi.
Et vous êtes parvenus en ce lieu-ci, et Sihon, Roi de Hesbon, et Hog, Roi de Basan, sont sortis au devant de nous pour nous combattre, et nous les avons battus.
8 Muka ƙwace ƙasarsu, muka ba da ita gādo ga mutanen Ruben, mutanen Gad, da kuma rabin mutanen Manasse.
Et avons pris leur pays, et l'avons donné en héritage aux Rubénites, aux Gadites, et à la demi Tribu de Manassé.
9 Saboda haka sai ku kiyaye, ku bi sharuɗan wannan alkawari, don ku yi nasara a cikin kome da kuke yi.
Vous garderez donc les paroles de cette alliance, et vous les ferez, afin que vous prospériez dans tout ce que vous ferez.
10 Yau, ga ku nan tsaye, dukanku a gaban Ubangiji Allahnku, shugabanninku da manyan mutanenku, dattawanku da hafsoshinku, da kuma dukan sauran mutanen Isra’ila,
Vous comparaissez tous aujourd'hui devant l'Eternel votre Dieu, les chefs de vos Tribus, vos Anciens, vos Officiers, et tout homme d'Israël;
11 tare da’ya’yanku da matanku, da baƙin da suke zama sansanoninku, har ma da waɗanda suke muku faskare, da waɗanda suke ɗiba muku ruwa.
Vos petits enfants, vos femmes, et ton étranger qui est au milieu de ton camp, depuis ton coupeur de bois jusqu'à ton puiseur d'eau;
12 Kuna tsaye a nan don ku yi alkawari da Ubangiji Allahnku, alkawarin da Ubangiji yake yi ta wurin rantsuwa da ku a wannan rana,
Afin que tu entres dans l'alliance de l'Eternel ton Dieu, laquelle il traite aujourd'hui avec toi, et dans l'exécration du serment qu'il te fait faire;
13 don yă mai da ku jama’arsa yau, shi kuwa yă zama Allahnku kamar yadda ya yi muku alkawari, da yadda kuma ya rantse wa kakanninku, Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.
Afin qu'il t'établisse aujourd'hui pour [être] son peuple, et qu'il te soit Dieu, ainsi qu'il t'a dit, et ainsi qu'il a juré à tes pères, Abraham, Isaac, et Jacob.
14 Ina yin wannan alkawari da rantsuwar, ba da ku kaɗai da
Et ce n'est pas seulement avec vous que je traite cette alliance, et cette exécration du serment que vous faites;
15 kuke tsattsaye a nan tare da mu a yau a gaban Ubangiji Allahnmu ba, amma har da waɗanda ba sa nan yau.
Mais c'est tant avec celui qui est ici avec nous aujourd'hui devant l'Eternel notre Dieu, qu'avec celui qui n'est point ici avec nous aujourd'hui.
16 Ku kanku kun san yadda muka yi zama a Masar, da yadda muka yi ta ratsawa ta tsakiyar al’ummai muka wuce.
Car vous savez comment nous avons demeuré au pays d'Egypte, et comment nous avons passé chez les nations, parmi lesquelles vous avez passé.
17 A cikinsu, kun ga siffofi masu banƙyama da gumaka na itace da dutse, na azurfa da zinariya.
Et vous avez vu leurs abominations, et leurs dieux de fiente, [les dieux] de bois et de pierre, d'argent et d'or qui sont parmi eux.
18 Kada zuciyar wani mutum, ko ta wata mata ko na wani iyali, ko wata kabila cikinku yau, ta bar bin Ubangiji Allahnku, tă koma ga bauta wa gumakan waɗannan al’ummai. Kada a sami wani tushe mai ba da’ya’ya masu dafi, masu ɗaci a cikinku.
[Prenez garde] qu'il n'y ait parmi vous ni homme, ni femme, ni famille, ni Tribu qui détourne aujourd'hui son cœur de l'Eternel notre Dieu, pour aller servir les dieux de ces nations, [et] qu'il n'y ait parmi vous quelque racine qui produise du fiel et de l'absinthe.
19 Idan kuma wani mutum ya ji kalmomi na wannan rantsuwa, ya kuma sa wa kansa albarka yana tunani cewa, “Ba abin da zai same ni, ko da na nace a taurinkaina.” Wannan zai jawo lalacewar dukan Isra’ila tare da kai.
Et qu'il n'arrive que quelqu'un entendant les paroles de cette exécration du serment que vous faites, ne se bénisse en son cœur, en disant: J'aurai la paix, quoique je vive selon que je l'ai arrêté en mon cœur; afin d'ajouter l'ivrognerie à l'altération.
20 Ubangiji ba zai gafarce shi ba, fushinsa da kishinsa za su ƙuna a kan wannan mutum. Dukan la’anonin da aka rubuta a wannan littafi za su fāɗo a kansa, Ubangiji kuwa zai shafe sunansa daga ƙarƙashin sama.
L'Eternel refusera de lui pardonner; la colère de l'Eternel et sa jalousie s'enflammeront alors contre cet homme-là, et toute l'exécration du serment que vous faites, laquelle est écrite dans ce livre, demeurera sur lui, et l'Eternel effacera le nom de cet homme de dessous les cieux.
21 Ubangiji zai ware shi daga dukan kabilan Isra’ila don yă hukunta shi bisa ga dukan la’anonin alkawarin da aka rubuta a wannan Littafin Doka.
Et l'Eternel le séparera de toutes les Tribus d'Israël pour son malheur, selon toutes les exécrations du serment de l'alliance qui est écrite dans ce livre de la Loi.
22 Tsararraki masu zuwa nan gaba, wato,’ya’yan da za su gāje ku, da baƙon da ya zo daga ƙasa mai nisa, za su ga annobar ƙasar, da cuce-cucen da Ubangiji ya buge ta da su.
Et la génération à venir, vos enfants qui viendront après vous, et le forain qui viendra d'un pays éloigné, diront lorsqu'ils verront les plaies de ce pays, et ses maladies, dont l'Eternel l'affligera;
23 Ƙasar gaba ɗaya za tă zama gishiri mai ƙuna marar amfani da kuma kibiritu, babu shuki, babu abin da yake tsirowa, babu itatuwan da suke girma a cikinta. Za tă zama kamar yadda aka hallaka Sodom da Gomorra, Adma da Zeboyim, waɗanda Ubangiji ya hallaka cikin zafin fushinsa.
Et que toute la terre de ce pays-là ne sera que soufre, que sel, et qu'embrasement, qu'elle ne sera point semée, et qu'elle ne fera rien germer, et que nulle herbe n'en sortira, ainsi qu'en la subversion de Sodome, et de Gomorrhe, et d'Adma, et de Tséboïm, lesquelles l'Eternel détruisit en sa colère et en sa fureur;
24 Dukan al’ummai za su yi tambaya su ce, “Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan ƙasa? Me ya jawo wannan fushi mai tsanani haka?”
Même toutes les nations diront: Pourquoi l'Eternel a-t-il fait ainsi à ce pays? Quelle est l'ardeur de cette grande colère?
25 Amsar kuwa za tă zama, “Wannan ya zama haka domin wannan mutane, sun yi watsi da alkawarin Ubangiji Allah na kakanninsu, alkawarin da ya yi da su sa’ad da ya fitar da su daga Masar.
Et on répondra: C'est à cause qu'ils ont abandonné l'alliance de l'Eternel le Dieu de leurs pères, laquelle il avait traitée avec eux quand il les fit sortir du pays d'Egypte.
26 Sun juya, suka bauta wa waɗansu alloli, suka rusuna musu, allolin da ba su sani ba, allolin da Ubangiji bai ba su ba.
Car ils s'en sont allés, et ont servi d'autres dieux, et se sont prosternés devant eux, devant ces dieux qu'ils n'avaient point connus, et aucun desquels ne leur avait rien donné.
27 Saboda haka fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan wannan ƙasa, har ya kawo dukan la’anoni da aka rubuta a wannan littafi a kanta.
A cause de cela la colère de l'Eternel s'est embrasée contre ce pays, pour faire venir sur lui toutes les malédictions écrites dans ce livre.
28 Cikin zafin fushi da babbar hasala Ubangiji ya tumɓuke su daga ƙasarsu, ya watsar da su cikin wata ƙasa dabam, kamar yadda suke a yau.”
Et l'Eternel les a arrachés de leur terre en sa colère, et en sa fureur, et en sa grande indignation, et les a chassés en un autre pays, comme [il paraît] aujourd'hui.
29 Ubangiji Allahnmu bai bayyana abubuwa na yanzu da na nan gaba ba, amma ya umarce mu mu kiyaye kalmomin dokar da ya ba mu, mu da kuma’ya’yanmu har abada.
Les choses cachées sont pour l'Eternel notre Dieu; mais les choses révélées sont pour nous et pour nos enfants à jamais, afin que nous fassions toutes les paroles de cette Loi.

< Maimaitawar Shari’a 29 >