< Maimaitawar Shari’a 29 >

1 Waɗannan su ne sharuɗan alkawarin da Ubangiji ya umarci Musa yă yi da Isra’ilawa a Mowab, wato, ban da alkawarin da ya yi da su a Dutsen Horeb.
To su riječi Saveza što ga propisa Jahve Mojsiju da ga sklopi s Izraelcima u zemlji moapskoj, povrh Saveza što ga je s njima sklopio na Horebu.
2 Sai Musa ya tara dukan Isra’ila, ya ce musu, Idanunku sun ga dukan abin da Ubangiji ya yi a Masar ga Fir’auna, ga kuma dukan shugabanninsa da kuma ga dukan ƙasarsa.
Mojsije sazva sav Izrael pa im reče: “Vidjeli ste na rođene oči sve što je Jahve učinio u zemlji egipatskoj faraonu, svim službenicima njegovim i svoj zemlji njegovoj:
3 Da idanunku kun ga waɗannan gwaje-gwaje, waɗannan alamu masu banmamaki, da al’ajabai masu girma.
velike kušnje što su ih vidjele tvoje oči, silne znakove i čudesa!
4 Duk da haka har wa yau Ubangiji bai ba ku hankalin ganewa, ko idanun da za su gani, ko kunnuwan da za su ji ba.
Ali vam ne dade Jahve do danas razuma da shvatite, očiju da vidite ni ušiju da čujete.
5 Shekaru arba’in da na jagorance ku cikin hamada, tufafinku ba su yage ba, haka kuwa takalman da suke a ƙafafunku.
Vodio sam vas pustinjom četrdeset godina; odjeća se na vama nije izderala niti su se sandale na vašim nogama raskidale.
6 Ba ku ci burodi ba, ba ku kuwa sha ruwan inabi, ko wani abu mai sa jiri ba. Ya yi haka don ku san cewa shi ne Ubangiji Allahnku.
Kruha niste jeli; vina ni drugoga opojnog pića niste pili, da biste znali da sam ja Jahve, Bog vaš.
7 Sa’ad da kuka kai wannan wuri, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan, suka fito don su yi yaƙi da mu, amma muka ci su da yaƙi.
Kad stigoste na novo mjesto, Sihon, kralj hešbonski, i Og, kralj bašanski, iziđoše pred nas u boj, ali smo ih potukli.
8 Muka ƙwace ƙasarsu, muka ba da ita gādo ga mutanen Ruben, mutanen Gad, da kuma rabin mutanen Manasse.
Zauzeli smo njihovu zemlju te je predali u baštinu Rubenovcima, Gadovcima i polovini plemena Manašeova.
9 Saboda haka sai ku kiyaye, ku bi sharuɗan wannan alkawari, don ku yi nasara a cikin kome da kuke yi.
Držite i vršite riječi ovog Saveza da uspijevate u svemu što poduzmete.
10 Yau, ga ku nan tsaye, dukanku a gaban Ubangiji Allahnku, shugabanninku da manyan mutanenku, dattawanku da hafsoshinku, da kuma dukan sauran mutanen Isra’ila,
Danas stojite svi pred Jahvom, Bogom svojim: vaši plemenski glavari, vaše starješine i vaši nadglednici, svi muževi Izraela,
11 tare da’ya’yanku da matanku, da baƙin da suke zama sansanoninku, har ma da waɗanda suke muku faskare, da waɗanda suke ɗiba muku ruwa.
djeca vaša, žene vaše i došljak koji je u tvome taboru - od onoga koji ti siječe drva do onoga koji ti nosi vodu -
12 Kuna tsaye a nan don ku yi alkawari da Ubangiji Allahnku, alkawarin da Ubangiji yake yi ta wurin rantsuwa da ku a wannan rana,
da stupite u Savez s Jahvom, Bogom svojim, u Savez zakletvom potvrđen, što ga Jahve, Bog tvoj, danas s tobom sklapa
13 don yă mai da ku jama’arsa yau, shi kuwa yă zama Allahnku kamar yadda ya yi muku alkawari, da yadda kuma ya rantse wa kakanninku, Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.
da danas od tebe učini svoj narod i da ti on bude Bog, kako ti je rekao i kako se zakleo tvojim ocima: Abrahamu, Izaku i Jakovu.
14 Ina yin wannan alkawari da rantsuwar, ba da ku kaɗai da
I ne sklapam danas ovaj Savez sa zakletvom samo s vama
15 kuke tsattsaye a nan tare da mu a yau a gaban Ubangiji Allahnmu ba, amma har da waɗanda ba sa nan yau.
nego i sa svakim koji danas stoji ovdje s nama pred Jahvom, Bogom našim, i sa svakim koji danas nije ovdje s nama.
16 Ku kanku kun san yadda muka yi zama a Masar, da yadda muka yi ta ratsawa ta tsakiyar al’ummai muka wuce.
Sami znate kako smo boravili u zemlji egipatskoj i kako smo prošli posred naroda kroz koje ste morali proći.
17 A cikinsu, kun ga siffofi masu banƙyama da gumaka na itace da dutse, na azurfa da zinariya.
Vidjeli ste njihove rugobe, njihove kumire od drveta i kamena, srebra i zlata što ih imaju.
18 Kada zuciyar wani mutum, ko ta wata mata ko na wani iyali, ko wata kabila cikinku yau, ta bar bin Ubangiji Allahnku, tă koma ga bauta wa gumakan waɗannan al’ummai. Kada a sami wani tushe mai ba da’ya’ya masu dafi, masu ɗaci a cikinku.
Neka ne bude među vama čovjeka ni žene, roda ni plemena kojemu bi se srce danas odvratilo od Jahve, Boga našega, pa da ide iskazivati štovanje bogovima onih naroda. Neka ne bude među vama korijena koji rađa otrovom i pelinom.
19 Idan kuma wani mutum ya ji kalmomi na wannan rantsuwa, ya kuma sa wa kansa albarka yana tunani cewa, “Ba abin da zai same ni, ko da na nace a taurinkaina.” Wannan zai jawo lalacewar dukan Isra’ila tare da kai.
Neka se nitko, čuvši riječi ovog prokletstva, ne nada blagoslovu kazujući u svome srcu: 'Bit će mi dobro ako poživim i po prohtjevima srca svoga. Nek' povodanj utaži žeđ!'
20 Ubangiji ba zai gafarce shi ba, fushinsa da kishinsa za su ƙuna a kan wannan mutum. Dukan la’anonin da aka rubuta a wannan littafi za su fāɗo a kansa, Ubangiji kuwa zai shafe sunansa daga ƙarƙashin sama.
Takvome neće Jahve nikad oprostiti, nego će se gnjev i ljubomornost Jahvina izliti na tog čovjeka, tako da će se sve prokletstvo zapisano u ovoj knjizi na nj oboriti te će Jahve izbrisati ime njegovo pod nebom.
21 Ubangiji zai ware shi daga dukan kabilan Isra’ila don yă hukunta shi bisa ga dukan la’anonin alkawarin da aka rubuta a wannan Littafin Doka.
Prema svim prokletstvima ovog Saveza, zapisanima u knjizi ovoga Zakona, Jahve će ga odstraniti, na njegovu propast, od svih plemena izraelskih.
22 Tsararraki masu zuwa nan gaba, wato,’ya’yan da za su gāje ku, da baƙon da ya zo daga ƙasa mai nisa, za su ga annobar ƙasar, da cuce-cucen da Ubangiji ya buge ta da su.
Kasniji naraštaj, sinovi vaši poslije vas, i stranci koji dođu iz daleke zemlje, kad vide zla ove zemlje i bolesti što će ih Jahve pustiti na nju, reći će:
23 Ƙasar gaba ɗaya za tă zama gishiri mai ƙuna marar amfani da kuma kibiritu, babu shuki, babu abin da yake tsirowa, babu itatuwan da suke girma a cikinta. Za tă zama kamar yadda aka hallaka Sodom da Gomorra, Adma da Zeboyim, waɗanda Ubangiji ya hallaka cikin zafin fushinsa.
'Sva je zemlja njegova samo sumpor i sol; niti se što sije niti što klija; nikakva travka na njoj ne raste; jednaka je srušenoj Sodomi i Gomori, Admi i Sebojimu, što ih Jahve sruši u svojoj ljutini i gnjevu.'
24 Dukan al’ummai za su yi tambaya su ce, “Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan ƙasa? Me ya jawo wannan fushi mai tsanani haka?”
I svi će narodi pitati: 'Zašto učini Jahve ovako ovoj zemlji? Kakva je morala biti žestina toga silnoga gnjeva?'
25 Amsar kuwa za tă zama, “Wannan ya zama haka domin wannan mutane, sun yi watsi da alkawarin Ubangiji Allah na kakanninsu, alkawarin da ya yi da su sa’ad da ya fitar da su daga Masar.
Onda će im se reći: 'Jer su ostavili Savez što ga je Jahve, Bog otaca njihovih, bio sklopio s njima kad ih je izveo iz zemlje egipatske;
26 Sun juya, suka bauta wa waɗansu alloli, suka rusuna musu, allolin da ba su sani ba, allolin da Ubangiji bai ba su ba.
i jer su otišli da iskazuju štovanje drugim bogovima i njima se klanjali, bogovima kojih nisu poznavali i kojih im on nije odredio.
27 Saboda haka fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan wannan ƙasa, har ya kawo dukan la’anoni da aka rubuta a wannan littafi a kanta.
Zato se Jahvin gnjev izlio na ovu zemlju i palo na nju sve prokletstvo zapisano u ovoj knjizi.
28 Cikin zafin fushi da babbar hasala Ubangiji ya tumɓuke su daga ƙasarsu, ya watsar da su cikin wata ƙasa dabam, kamar yadda suke a yau.”
Jahve ih je iščupao iz njihove zemlje u ljutini, srdžbi i velikom gnjevu te ih bacio u drugu zemlju. Tako je i danas.'
29 Ubangiji Allahnmu bai bayyana abubuwa na yanzu da na nan gaba ba, amma ya umarce mu mu kiyaye kalmomin dokar da ya ba mu, mu da kuma’ya’yanmu har abada.
Što je sakriveno, pripada Jahvi, Bogu našemu, a objava nama i sinovima našim zauvijek da vršimo sve riječi ovoga Zakona.

< Maimaitawar Shari’a 29 >