< Maimaitawar Shari’a 29 >

1 Waɗannan su ne sharuɗan alkawarin da Ubangiji ya umarci Musa yă yi da Isra’ilawa a Mowab, wato, ban da alkawarin da ya yi da su a Dutsen Horeb.
Ето думите на завета, който Господ заповяда на Моисея да направи с израилтяните в Моавската земя, освен завета, който направи с тях в Хорив.
2 Sai Musa ya tara dukan Isra’ila, ya ce musu, Idanunku sun ga dukan abin da Ubangiji ya yi a Masar ga Fir’auna, ga kuma dukan shugabanninsa da kuma ga dukan ƙasarsa.
Моисей повика целия Израил и им каза: Вие видяхте всичко що направи Господ пред очите ви в Египетската земя, на Фараона и на всичките му слуги, и на цялата му земя;
3 Da idanunku kun ga waɗannan gwaje-gwaje, waɗannan alamu masu banmamaki, da al’ajabai masu girma.
големите изпитни, които очите ти видяха, знаменията и ония големи чудеса;
4 Duk da haka har wa yau Ubangiji bai ba ku hankalin ganewa, ko idanun da za su gani, ko kunnuwan da za su ji ba.
но до тоя ден Господ не ви даде сърце за да разбирате, очи за да виждате и уши за да слушате.
5 Shekaru arba’in da na jagorance ku cikin hamada, tufafinku ba su yage ba, haka kuwa takalman da suke a ƙafafunku.
А Аз ви дадох за четиридесет години по пустинята, през което време дрехите ви не овехтяха на вас, и обущата ни на един от вас не овехтяха на ногата ти,
6 Ba ku ci burodi ba, ba ku kuwa sha ruwan inabi, ko wani abu mai sa jiri ba. Ya yi haka don ku san cewa shi ne Ubangiji Allahnku.
хляб не ядохте, и вино и спиртни пития не пихте, за да знаете, че Аз съм Господ вашият Бог.
7 Sa’ad da kuka kai wannan wuri, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan, suka fito don su yi yaƙi da mu, amma muka ci su da yaƙi.
И когато дойдохте на това място есевонският цар Сион и васанският цар Ог излезе против нас на бой; а ние ги поразихме,
8 Muka ƙwace ƙasarsu, muka ba da ita gādo ga mutanen Ruben, mutanen Gad, da kuma rabin mutanen Manasse.
завладяхме земята им, и я дадохме за наследство на рувимците, на гадците и на половината от Манасиевото племе.
9 Saboda haka sai ku kiyaye, ku bi sharuɗan wannan alkawari, don ku yi nasara a cikin kome da kuke yi.
Пазете, прочее, думите на тоя завет и изпълнявайте ги, за да успявате във всичко що правите.
10 Yau, ga ku nan tsaye, dukanku a gaban Ubangiji Allahnku, shugabanninku da manyan mutanenku, dattawanku da hafsoshinku, da kuma dukan sauran mutanen Isra’ila,
Днес вие всички стоите пред Господа вашия Бог, - началниците на племената ви, старейшините ви, надзирателите ви, всичките Израилеви мъже,
11 tare da’ya’yanku da matanku, da baƙin da suke zama sansanoninku, har ma da waɗanda suke muku faskare, da waɗanda suke ɗiba muku ruwa.
чадата ви, жените и чужденецът, който е всред стана ти, от дървосечеца ти до водоносеца ти,
12 Kuna tsaye a nan don ku yi alkawari da Ubangiji Allahnku, alkawarin da Ubangiji yake yi ta wurin rantsuwa da ku a wannan rana,
за да встъпиш в завета на Господа твоя Бог и в клетвата, която Господ твоят Бог прави днес с тебе,
13 don yă mai da ku jama’arsa yau, shi kuwa yă zama Allahnku kamar yadda ya yi muku alkawari, da yadda kuma ya rantse wa kakanninku, Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.
за да те утвърди днес на Свои люде, и Той да ти бъде Бог, според както ти е рекъл и както се е клел на бащите ти, на Авраама, на Исаака и на Якова.
14 Ina yin wannan alkawari da rantsuwar, ba da ku kaɗai da
И аз не правя тоя завет и тая клетва само с вас,
15 kuke tsattsaye a nan tare da mu a yau a gaban Ubangiji Allahnmu ba, amma har da waɗanda ba sa nan yau.
но както с ония, които днес стоят тук с нас пред Господа нашия Бог, така и с ония, които днес не са тук с нас;
16 Ku kanku kun san yadda muka yi zama a Masar, da yadda muka yi ta ratsawa ta tsakiyar al’ummai muka wuce.
(защото вие знаехте как живяхме в Египетската земя, и как минахме всред народите през които пропътувахме;
17 A cikinsu, kun ga siffofi masu banƙyama da gumaka na itace da dutse, na azurfa da zinariya.
и видяхме мерзостите им, и дървените им и каменни, сребърни и златни кумири, които са между тях);
18 Kada zuciyar wani mutum, ko ta wata mata ko na wani iyali, ko wata kabila cikinku yau, ta bar bin Ubangiji Allahnku, tă koma ga bauta wa gumakan waɗannan al’ummai. Kada a sami wani tushe mai ba da’ya’ya masu dafi, masu ɗaci a cikinku.
тъй щото да няма между вас мъж или жена, семейство или племе, чието сърце да се отклонява днес от Господа нашия Бог, за да иде да служи на боговете на ония народи; тъй щото да няма между вас корен, който да ражда отрова и пелин,
19 Idan kuma wani mutum ya ji kalmomi na wannan rantsuwa, ya kuma sa wa kansa albarka yana tunani cewa, “Ba abin da zai same ni, ko da na nace a taurinkaina.” Wannan zai jawo lalacewar dukan Isra’ila tare da kai.
та, когато чуе думите на тая клетва, да ласкае себе си в сърцето си и да рече: Аз ще имам мир, ако и да ходя с упорито сърце и притурям пиянство на жаждата.
20 Ubangiji ba zai gafarce shi ba, fushinsa da kishinsa za su ƙuna a kan wannan mutum. Dukan la’anonin da aka rubuta a wannan littafi za su fāɗo a kansa, Ubangiji kuwa zai shafe sunansa daga ƙarƙashin sama.
Бог няма да се умилостиви на него, но изведнъж гневът на Господа и ревността Му ще пламнат против тоя човек; и всяка проклетия, която е написана в тая книга, ще падне на него, и Господ ще изличи името му под небето.
21 Ubangiji zai ware shi daga dukan kabilan Isra’ila don yă hukunta shi bisa ga dukan la’anonin alkawarin da aka rubuta a wannan Littafin Doka.
Господ ще го отдели от всичките Израилеви племена за погибел, според всичките проклетии на завета написан в тая книга на закона.
22 Tsararraki masu zuwa nan gaba, wato,’ya’yan da za su gāje ku, da baƙon da ya zo daga ƙasa mai nisa, za su ga annobar ƙasar, da cuce-cucen da Ubangiji ya buge ta da su.
А идещото поколение, чадата ви, които ще настанат подир вас, и чужденецът, който дойде от далечна земя, когато видят язвите нанесени на оная земя и болестите, с които Господ я е направил да боледува, ще кажат:
23 Ƙasar gaba ɗaya za tă zama gishiri mai ƙuna marar amfani da kuma kibiritu, babu shuki, babu abin da yake tsirowa, babu itatuwan da suke girma a cikinta. Za tă zama kamar yadda aka hallaka Sodom da Gomorra, Adma da Zeboyim, waɗanda Ubangiji ya hallaka cikin zafin fushinsa.
Цялата земя е изгорена със сяра и със сол, та нито се сее нито произраства, и никаква трева не никне на нея, както при съсипването на Содом и Гомор, на Адам и Севоим, които Господ съсипа в гнева Си и в яростта Си.
24 Dukan al’ummai za su yi tambaya su ce, “Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan ƙasa? Me ya jawo wannan fushi mai tsanani haka?”
Всичките, народи ще кажат: Защо направи Господ така на тая земя? Що значи яростта на тоя голям гняв?
25 Amsar kuwa za tă zama, “Wannan ya zama haka domin wannan mutane, sun yi watsi da alkawarin Ubangiji Allah na kakanninsu, alkawarin da ya yi da su sa’ad da ya fitar da su daga Masar.
Тогава ще им думат: Защото оставиха завета на Господа Бога на бащите си, който Той направи с тях, когато ги изведе из Египетската земя,
26 Sun juya, suka bauta wa waɗansu alloli, suka rusuna musu, allolin da ba su sani ba, allolin da Ubangiji bai ba su ba.
и отидоха та служиха на други богове и им се поклониха, богове, които не знаеха, и които Той не бе им дал,
27 Saboda haka fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan wannan ƙasa, har ya kawo dukan la’anoni da aka rubuta a wannan littafi a kanta.
за това пламна яростта на Господа против тая земя, за да докара на нея всичките проклетии, които са написани в тая книга.
28 Cikin zafin fushi da babbar hasala Ubangiji ya tumɓuke su daga ƙasarsu, ya watsar da su cikin wata ƙasa dabam, kamar yadda suke a yau.”
И Господ ги изкорени от земята им с гняв, с ярост и с голямо негодувание, и ги хвърли в друга земя където са днес.
29 Ubangiji Allahnmu bai bayyana abubuwa na yanzu da na nan gaba ba, amma ya umarce mu mu kiyaye kalmomin dokar da ya ba mu, mu da kuma’ya’yanmu har abada.
Скритото принадлежи на Господа нашия Бог, а откритото принадлежи на нас и на чадата ни до века, за да изпълняваме всичките думи на тоя закон.

< Maimaitawar Shari’a 29 >