< Maimaitawar Shari’a 28 >
1 In kun yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku, kuka kuma lura, kuka bi dukan umarnan da na ba ku a yau, Ubangiji Allahnku zai sa ku bisa dukan al’ummai a duniya.
“Eğer Tanrınız RAB'bin sözünü iyice dinler ve bugün size ilettiğim bütün buyruklarına uyarsanız, Tanrınız RAB sizi yeryüzündeki bütün uluslardan üstün kılacaktır.
2 Dukan waɗannan albarku za su sauko muku, su zama naku, in kuka yi biyayya ga Ubangiji Allahnku.
Tanrınız RAB'bin sözünü dinlerseniz, şu bereketler üzerinize gelecek ve sizinle olacak:
3 Za ku zama masu albarka a cikin birni, za ku kuma zama masu albarka har a ƙauye.
“Kentte de tarlada da kutsanacaksınız.
4 ’Ya’yanku za su zama masu albarka, haka ma hatsin gonakinku da kuma’ya’yan dabbobinku, wato,’ya’yan shanu da’yan tumakinku.
“Rahminizin meyvesi kutsanacak. Toprağınızın ürünü, hayvanlarınızın dölü –sığırlarınızın buzağıları, sürülerinizin kuzuları– bereketli olacak.
5 Za a albarkaci kwandonku da kwanon kwaɓan kullunku.
“Sepetiniz ve hamur tekneniz bereketli olacak.
6 Za ku zama masu albarka sa’ad da kuka shiga, za ku kuma zama masu albarka sa’ad da kuka fita.
“İçeri girdiğinizde de dışarı çıktığınızda da kutsanacaksınız.
7 A gabanku, Ubangiji zai sa ku fatattaki abokan gāban da za su taso suna gāba da ku. Ta hanya guda za su auka muku, amma ta hanyoyi bakwai za su gudu daga gabanku.
“RAB size saldıran düşmanlarınızı önünüzde bozguna uğratacak. Onlar size bir yoldan saldıracak, ama önünüzden yedi yoldan kaçacaklar.
8 Ubangiji zai aika da albarka a rumbunanku da kuma a bisa kome da kuka sa hannunku a kai. Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a ƙasar da yake ba ku.
“RAB'bin buyruğuyla ambarlarınız dolu olacak. El attığınız her işte RAB sizi kutsayacak. Tanrınız RAB size vereceği ülkede sizi kutsayacak.
9 Ubangiji zai kafa ku kamar mutanensa masu tsarki, kamar yadda ya yi alkawari da rantsuwa, in kun kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi tafiya a hanyoyinsa.
“Tanrınız RAB'bin buyruklarına uyar, O'nun yollarında yürürseniz, RAB size içtiği ant uyarınca sizi kendisi için kutsal bir halk olarak koruyacaktır.
10 Sa’an nan dukan mutane a duniya za su ga cewa ana kiranku da sunan Ubangiji, za su kuwa ji tsoronku.
Yeryüzündeki bütün uluslar RAB'be ait olduğunuzu görecek, sizden korkacaklar.
11 Ubangiji zai azurta ku sosai, a’ya’yan cikinku, a’ya’yan dabbobinku da kuma a hatsin gonarku, a cikin ƙasar da ya rantse wa kakanninku zai ba ku.
RAB atalarınıza ant içerek size söz verdiği ülkede bolluk içinde yaşamanızı sağlayacak: Rahminizin meyvesi kutsanacak; hayvanlarınızın yavruları, toprağınızın ürünü verimli olacak.
12 Ubangiji zai buɗe sammai, wurin ajiyarsa mai yalwa, don yă aika da ruwan sama a gonarku a lokacinsa, yă kuma albarkaci dukan aikin hannuwanku. Za ku ba wa al’ummai masu yawa rance, amma ba za ku karɓa bashi daga wurin wani ba.
RAB ülkenize yağmuru zamanında yağdırmak ve bütün emeğinizi verimli kılmak için göklerdeki zengin hazinesini açacak. Birçok ulusa ödünç vereceksiniz; siz ödünç almayacaksınız.
13 Ubangiji zai sa ku zama kai, ba wutsiya ba. In kun mai da hankali ga umarnan Ubangiji Allahnku da nake ba ku a wannan rana, kuka kuma lura, kuka bi su, kullum za ku kasance a bisa, ba a ƙasa ba.
RAB sizi kuyruk değil baş yapacak. Eğer bugün size ilettiğim Tanrınız RAB'bin buyruklarını dinler, onlara iyice uyarsanız, altta değil, her zaman üstte olacaksınız.
14 Kada ku kauce zuwa dama ko zuwa hagu daga umarnan da na ba ku a yau, har ku bi waɗansu alloli kuna yin musu sujada.
Bugün size ilettiğim buyrukların dışına çıkmayacak, başka ilahların ardınca gitmeyecek, onlara tapmayacaksınız.”
15 Amma fa, in ba ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku ba, ba ku kuma lura kun bi dukan umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau ba, dukan la’anan nan za su zo a bisanku, su kuma same ku.
“Ama Tanrınız RAB'bin sözünü dinlemez, bugün size ilettiğim buyrukların, kuralların hepsine uymazsanız, şu lanetler üzerinize gelecek ve size ulaşacak:
16 Za ku zama la’anannu a birni da kuma a ƙauye.
“Kentte de tarlada da lanetli olacaksınız.
17 Za a la’anta kwandonku da kwanon kwaɓan kullunku.
“Sepetiniz ve hamur tekneniz lanetli olacak.
18 Za a la’anta’ya’yan cikinku, haka ma hatsin gonarku, da’ya’yan shanunku da’yan tumakinku.
“Rahminizin meyvesi, toprağınızın ürünü, sığırlarınızın buzağıları, sürülerinizin kuzuları lanetli olacak.
19 Za a la’anta ku sa’ad da kuka shiga da sa’ad da kuka fita.
“İçeri girdiğinizde lanetli olacaksınız; dışarı çıktığınızda da lanetli olacaksınız.
20 Ubangiji zai aiko muku da la’ana, da ruɗewa, da damuwa cikin dukan abin da za ku yi, har ya hallaka ku, ku lalace da sauri saboda mugayen ayyukanku, domin kuma kuka rabu da ni.
“RAB'be sırt çevirmekle yaptığınız kötülükler yüzünden el attığınız her işte O sizi lanete uğratacak, şaşkına çevirecek, paylayacak. Sonunda üzerinize yıkım gelecek ve çabucak yok olacaksınız.
21 Ubangiji zai aiko muku da annoba wadda za tă manne muku, tă cinye ku cikin ƙasar da za ku shiga, ku mallake ta.
RAB, mülk edinmek için gideceğiniz ülkede sizi yok edinceye dek salgın hastalıkla cezalandıracak.
22 Ubangiji zai buga ku da cuta mai lalacewa, da zazzaɓi, da ƙuna, da zafin rana, da fāri, da burtuntuna, da fumfuna, waɗanda za su azabtar da ku sai kun hallaka.
Veremle, sıtmayla, iltihapla, yakıcı sıcaklıkla, kuraklıkla, samyeliyle, küfle cezalandıracak. Siz yok oluncaya dek bunlar sizi kovalayacak.
23 Girgijen da yake bisanku zai zama tagulla, ƙasar da take ƙarƙashinku za tă zama ƙarfe.
Başınızın üstündeki gök tunç, ayağınızın altındaki yer demir olacak.
24 Ubangiji zai juye ruwan saman ƙasarku yă zama ƙura da gari; zai sauko daga gizagizai har sai kun hallaka.
RAB siz yok oluncaya dek gökten yağmur yerine ülkenize toz ve kum yağdıracak.
25 Ubangiji zai sa a rinjaye ku a gaban abokan gābanku. Ta hanya guda za ku auka musu, amma ta hanyoyi bakwai za ku gudu daga gabansu. Za ku zama abin ƙi ga dukan mulkokin duniya.
“RAB sizi düşmanlarınızın önünde bozguna uğratacak. Onlara bir yoldan saldıracak, ama önlerinden yedi yoldan kaçacaksınız. Yeryüzündeki bütün uluslar için dehşet verici bir örnek olacaksınız.
26 Gawawwakinku za su zama abincin dukan tsuntsayen sarari da namun duniya, ba kuwa wanda zai kore su.
Ölüleriniz bütün kuşlara, yabanıl hayvanlara yem olacak; onları korkutup kaçıran kimse olmayacak.
27 Ubangiji zai buge ku da maruran Masar, da ƙazuwa, da kuma ƙaiƙayi waɗanda ba za su warke ba
RAB sizi iyileşemeyeceğiniz Mısır çıbanıyla, urlarla, kaşıntıyla, uyuzla vuracak.
28 Ubangiji zai buge ku da hauka, makanta, da rikicewar hankali.
RAB sizi delilikle, körlükle, şaşkınlıkla cezalandıracak.
29 Da tsakar rana za ku riƙa lallubawa kamar makaho. Za ku zama marasa nasara a cikin kome da kuka yi; kowace rana za a zalunce ku, a kuma yi muku ƙwace, ba tare da wani ya cece ku ba.
Öğle vakti körlerin karanlıkta el yordamıyla yürüdüğü gibi yürüyeceksiniz. Yaptığınız her şeyde başarısız olacak, sürekli sıkıştırılacak, yağmalanacaksınız. Sizi kurtaran olmayacak.
30 Za ku yi tashin yarinya, amma wani ne zai ɗauke ta yă kwana da ita. Za ku gina gida amma wani ne zai zauna a ciki. Za ku shuka inabi, amma ba za ku ma fara jin daɗin’ya’yansa ba.
“Bir kızla nişanlanacaksınız, ama başka biri onunla yatacak. Ev yapacak ama içinde oturmayacaksınız. Bağ dikecek ama üzümünü toplamayacaksınız.
31 Za a yanka sanku a idanunku, amma ba za ko ci wani abu a cikinsa ba. Za a ƙwace jakinku ƙiri-ƙiri, amma ba za a mayar muku da shi ba. Za a ba da tumakinku ga abokan gābanku, kuma ba kowa da zai cece su.
Öküzünüz gözünüzün önünde kesilecek ama etini yemeyeceksiniz. Eşeğiniz zorla sizden alınacak, geri getirilmeyecek. Davarlarınız düşmanlarınıza verilecek. Sizi kurtaran olmayacak.
32 Za a ba da’ya’yanku maza da mata ga wata al’umma, za ku kuma yi ta zuba idanunku kuna neman su kullayaumi, amma a banza, domin ba ku da ikon yin kome.
Oğullarınız, kızlarınız gözlerinizin önünde başka bir ulusa verilecek. Her gün onları gözlemekten gözlerinizin gücü tükenecek. Elinizden bir şey gelmeyecek.
33 Mutanen da ba ku sani ba za su ci kayan gonarku da amfanin wahalarku, za a yi ta cucinku, ana kuma danne ku kullum.
Tanımadığınız bir halk toprağınızın ürününü ve bütün emeğinizi yiyecek. Sürekli sıkıştırılacak, ezileceksiniz.
34 Abubuwan da za ku gani za su sa ku yi hauka.
Gözlerinizle gördükleriniz sizi çıldırtacak.
35 Ubangiji zai buge gwiwoyinku da ƙafafunku da marurai masu zafi da ba za a iya warkar da su ba, za su yaɗu daga tafin ƙafafu zuwa bisa kanku.
RAB dizlerinizi, bacaklarınızı tepeden tırnağa iyileşmeyen ağrılı çıbanlarla vuracak.
36 Ubangiji zai kore ku, ku da sarkin da kuka naɗa a bisanku zuwa al’ummar da ku, ko kakanninku ba su sani ba. A can za ku yi wa waɗansu alloli sujada, allolin itace da na dutse.
“RAB sizi ve başınıza atayacağınız kralı sizin de atalarınızın da bilmediği bir ulusa sürecek. Orada ağaçtan, taştan yapılmış başka ilahlara tapacaksınız.
37 Za ku zama abin ƙi, abin dariya, da kuma abin habaici ga dukan al’ummai inda Ubangiji zai kore ku zuwa.
RAB'bin sizi süreceği bütün uluslar başınıza gelenlerden dehşete düşecek; sizi aşağılayacak, sizinle eğlenecekler.
38 Za ku shuka iri da yawa a gona, amma za ku girbe kaɗan, domin fāra za su cinye su.
“Çok tohum ekecek, ama az toplayacaksınız. Çünkü ürününüzü çekirge yiyecek.
39 Za ku shuka inabi ku kuma yi musu banƙasa, amma ba za ku sha ruwan inabin ba, domin tsutsotsi za su cinye su.
Bağlar dikecek, bakımını yapacak, ama şarap içmeyecek, üzüm toplamayacaksınız. Onları kurt yiyecek.
40 Za ku kasance da itatuwan zaitun ko’ina a ƙasarku, amma ba za ku yi amfani da mansu ba, domin’ya’yan zaitun za su kakkaɓe.
Ülkenizin her yerinde zeytinlikleriniz olacak, ama zeytinyağı sürünmeyeceksiniz. Zeytin ağaçlarınız ürününü yere dökecek.
41 Za ku haifi’ya’ya maza da mata, amma za su zama naku ba, domin za a kai su bauta.
Oğullarınız, kızlarınız olacak, ama sizinle kalmayacaklar, sürgüne gönderilecekler.
42 Tarin fāra za su mamaye dukan itatuwanku da kuma hatsin gonarku.
Bütün ağaçlarınızı, toprağınızın ürününü çekirgeler yiyecek.
43 Baƙin da suke tare da ku, za su yi ta ƙaruwa, ku kuwa za ku yi ta komawa baya-baya.
“Aranızdaki yabancılar yükseldikçe yükselecek, sizse alçaldıkça alçalacaksınız.
44 Za su ba ku bashi, amma ba za ku ba su bashi ba. Za su zama kai, ku kuwa za ku zama wutsiya.
O sana ödünç verecek, ama sen ona ödünç vermeyeceksin. O baş, sen kuyruk olacaksın.
45 Dukan waɗannan la’anoni za su sauko a kanku. Za su bi ku, su same ku, sai an hallaka ku, domin ba ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma kiyaye umarnai da ƙa’idodin da ya ba ku ba.
“Bütün bu lanetler başınıza yağacak. Yok oluncaya dek sizi kovalayacak ve size erişecek. Çünkü Tanrınız RAB'bin sözünü dinlemediniz, size verdiği buyrukları, kuralları yerine getirmediniz.
46 Za su zama alamu da al’ajabi gare ku da kuma zuriyarku har abada.
Bu lanetler siz ve soyunuz için sonsuza dek bir belirti, şaşılası bir olay olarak kalacak.
47 Gama ba ku bauta wa Ubangiji Allahnku da farin ciki da kuma murna a lokacin wadata ba,
Madem bolluk zamanında Tanrınız RAB'be sevinçle, hoşnutlukla kulluk etmediniz,
48 saboda haka a cikin yunwa da ƙishirwa, cikin tsiraici da mugun talauci, za ku bauta wa abokan gāban da Ubangiji ya aiko muku. Zai sa karkiyar ƙarfe a wuyanku har sai ya hallaka ku ƙaf.
RAB'bin üzerinize göndereceği düşmanlara kölelik edeceksiniz. Aç, susuz, çıplak kalacaksınız; her şeye gereksinim duyacaksınız. RAB sizi yok edinceye dek boynunuza demir boyunduruk vuracak.
49 Ubangiji zai kawo al’umma daga nesa, daga iyakar duniya, ta sauko a kanku kamar gaggafa, al’ummar da ba ku san yarenta ba,
“RAB uzaktan, dünyanın öbür ucundan bir ulusu –dilini bilmediğiniz bir ulusu, yaşlılara saygı, küçüklere sevgi beslemeyen acımasız bir ulusu– birden çullanan bir kartal gibi başınıza getirecek.
50 al’umma mai zafin hali wadda ba ta ba wa tsofaffi girma, kuma ba ta tausayin yara.
51 Za su cinye’ya’yan dabbobinku da hatsin gonarku sai an hallaka ku. Ba za su rage ko ƙwayar hatsi, ko sabon ruwan inabi, ko mai ba, ba kuwa za a bar’yan tumakinku ba, sai an lalatar da ku.
Siz yok oluncaya dek hayvanlarınızın yavrularını, toprağınızın ürününü yiyip bitirecekler. Size ne tahıl, ne şarap, ne zeytinyağı, ne sığırlarınızın buzağılarını, ne de sürülerinizin kuzularını bırakacaklar; ta ki, siz ortadan kalkıncaya dek.
52 Za su kuwa kewaye ku a dukan garuruwanku, har sai katangarku masu tsayi wadda kuke dogara gare su, sun fāɗi ko’ina a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.
Güvendiğiniz yüksek, dayanıklı surlar yerle bir oluncaya dek ülkenizdeki bütün kentlerde sizi kuşatacaklar. Tanrınız RAB'bin size verdiği ülkedeki bütün kentleri kuşatacaklar.
53 Saboda wahalar da abokan gābanku za su gasa muku a lokacin kwanto, za ku ci’ya’yan cikinku, naman’ya’yanku maza da mata waɗanda Ubangiji Allahnku ya ba ku.
“Kuşatma sırasında düşmanınızın vereceği sıkıntıdan rahminizin meyvesini, Tanrınız RAB'bin size verdiği oğulların, kızların etini yiyeceksiniz.
54 Kai, har da mutumin da ya fi hankali da kuma kirki a cikinku, ba zai ji tausayi ɗan’uwansa, ko matar da yake ƙauna, ko’ya’yansa da suka ragu ba,
Aranızdaki en yumuşak, en duyarlı adam bile öz kardeşine, sevdiği karısına, sağ kalan çocuklarına acımayacak;
55 ba kuwa zai ba waninsu wani naman’ya’yansa da yake ci ba. Gama dukan abin da ya rage masa ke nan saboda wahalar da abokan gābanku za su gasa muku a lokacin da ake kwanton wa dukan biranenku.
yediği çocuklarının etini onların hiçbiriyle paylaşmayacak. Çünkü düşmanın kuşatma sırasında sizi sıkıştırması yüzünden kentlerinizde hiç yiyecek kalmayacak.
56 Mace mafi hankali da kuma kirki a cikinku, kai, mafi hankali da kirki da ba ta ma karambanin taɓa ƙasa da tafin ƙafarta, za tă hana wa mijinta da take ƙauna, da kuma ɗanta, ko’yarta abinci.
Aranızda en yumuşak, en duyarlı kadın –yumuşaklığından ve duyarlılığından ayağının tabanını yere basmak istemeyen kadın– bile sevdiği kocasından, öz oğlundan, kızından, plasentayı ve doğuracağı çocukları esirgeyecek. Çünkü kuşatma sırasında düşmanın kentlerinizde size vereceği sıkıntıdan, yokluktan onları gizlice yiyecek.
57 A ɓoye za tă ci mahaifar da take biyo bayan ta haihu, da’ya’yan da za tă haifa, saboda ba ta da wani abinci lokacin da abokan gābanku za su kewaye garuruwanku da yaƙi mai tsanani.
58 In ba ku lura kuka bi dukan kalmomi wannan doka, waɗanda an rubuta a wannan littafi ba, ba ku kuma girmama wannan suna mai ɗaukaka da kuma mai banrazana na Ubangiji Allahnku ba,
“Bu kitapta yazılı yasanın bütün sözlerine uymaz, Tanrınız RAB'bin yüce ve heybetli adından korkmazsanız,
59 Ubangiji zai aika da annoba masu zafi a kanku da zuriyarku, masifu masu zafi waɗanda za su daɗe, da mugayen cututtuka waɗanda ba sa kawuwa.
RAB sizi ve soyunuzu korkunç belalarla, büyük ve sürekli belalarla, ağır, iyileşmez hastalıklarla vuracak.
60 Zai kawo muku dukan cututtukan Masar da kuke tsoro, za su kuwa manne muku.
Sizi ürküten Mısır'ın bütün hastalıklarını yeniden başınıza getirecek; size yapışacaklar.
61 Ubangiji kuma zai kawo muku kowane irin ciwo da masifar da ba a rubuta a cikin wannan Littafin Doka ba, har sai an hallaka ku.
Siz yok oluncaya dek RAB bu Yasa Kitabı'nda yazılmamış her türlü hastalığı ve belayı da başınıza getirecek.
62 Ku da kuke da yawa kamar taurari a sarari za ku ragu ku zama kaɗan, domin ba ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku ba.
Gökteki yıldızlar kadar çok olan sizler, sayıca az bırakılacaksınız. Çünkü Tanrınız RAB'bin sözüne kulak vermediniz.
63 Kamar yadda ya gamshi Ubangiji ya sa kuka yi arziki kuka kuma ƙaru, haka zai gamshe shi yă lalatar yă kuma hallaka ku. Za a tumɓuke ku daga ƙasar da kuke shiga ku mallaka.
Size iyilik yapmak, sizi çoğaltmak RAB'bi nasıl sevindirdiyse, sizi yıkmak ve yok etmek de öyle sevindirecektir. Mülk edinmek için gideceğiniz ülkeden sökülüp atılacaksınız.
64 Sa’an nan Ubangiji zai watsar da ku cikin dukan al’ummai, daga wannan bangon duniya zuwa wancan. A can za ku bauta waɗansu alloli, allolin itace da na dutse, waɗanda ko ku, ko kakanninku, ba ku sani ba.
“RAB sizi dünyanın bir ucundan öbür ucuna, bütün halklar arasına dağıtacak. Orada sizin de atalarınızın da tanımadığı, ağaçtan ve taştan yapılmış başka ilahlara tapacaksınız.
65 A cikin waɗancan al’ummai ba za ku sami hutu ba, ba wurin hutu wa tafin ƙafanku. A can Ubangiji zai sa fargaba a zuciyarku, yă sa idanunku su lalace, ranku zai yi suwu.
Bu uluslar arasında ne esenliğiniz ne de dinlenecek bir yeriniz olacak. Orada RAB size titreyen yürekler, umutsuzluk ve bakmaktan yorulmuş gözler verecek.
66 Za ku yi zama cikin damuwa kullum, cike da tsoro, dare da rana, ba tabbacin abin da zai faru da ranku.
Sürekli can kaygısı içinde yaşayacaksınız. Gece gündüz dehşet içinde olacaksınız. Yaşamınızın güvenliği olmayacak.
67 Da safe za ku ce, “Da ma yamma ne!” Da yamma kuma ku ce, “Da ma safiya ce!” Saboda tsoron da ya cika zukatanku da kuma abubuwan da idanunku za su gani.
Yüreğinizi kaplayan dehşet ve gözlerinizin gördüğü olaylar yüzünden, sabah, ‘Keşke akşam olsa!’, akşam, ‘Keşke sabah olsa!’ diyeceksiniz.
68 Ubangiji zai komar da ku cikin jiragen ruwa zuwa Masar, tafiyar da na ce kada ku ƙara yi. A can za ku ba da kanku don sayarwa ga abokan gābanku a matsayin bayi maza da mata, amma ba wanda zai saye ku.
Bir daha görmeyeceksiniz dediğim yoldan RAB sizi gemilerle Mısır'a geri gönderecek. Orada erkek ve kadın köle olarak kendinizi düşmanlarınıza satmaya kalkışacaksınız; ama satın alan olmayacak.”