< Maimaitawar Shari’a 27 >

1 Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
Och Mose, samt med de äldsta i Israel, böd folkena, och sade: Behåller all de bud, som jag bjuder eder i dag.
2 Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
Och på den tiden, när I öfver Jordan dragen in i landet, som Herren din Gud dig gifvandes varder, skall du uppresa stora stenar, och plåstra dem med kalk;
3 Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
Och derpå skrifva all dessa lagsens ord, när du deröfver kommer; på det du skall komma i landet, som Herren din Gud dig gifva skall, ett land der mjölk och hannog uti flyter; såsom Herren dina fäders Gud dig sagt hafver.
4 Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
När I nu gån öfver Jordan, så skolen I sådana stenar uppresa, om hvilka jag eder i dag bjuder, på det berget Ebal, och plåstra dem med kalk;
5 Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
Och skall dersammastäds uppbygga Herranom dinom Gud ett altare af sten, der intet jern kommer vid.
6 Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
Af helom stenom skall du bygga det altaret Herranom dinom Gud, och offra deruppå bränneoffer Herranom dinom Gud;
7 Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
Och skall offra tackoffer, och dersammastäds äta, och vara glad för Herranom dinom Gud;
8 Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
Och skall skrifva på stenarna all dessa lagsens ord, klarliga och ljusliga.
9 Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
Och Mose, samt med Presterna Leviterna, talade med hela Israel, och sade: Märk och hör till, Israel; på denna dagen äst du vorden Herrans dins Guds folk;
10 Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
Att du skall lydig vara Herrans dins Guds röst, och göra efter hans bud och rätter, som jag bjuder dig i dag.
11 A wannan rana Musa ya umarce mutane,
Och Mose böd folkena på samma dagen, och sade:
12 Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
Desse skola stå på det berget Grisim, till att välsigna folket, när I öfver Jordan gångne ären: Simeon, Levi, Juda, Isaschar, Joseph och BenJamin.
13 Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
Och desse skola stå på det berget Ebal, till att förbanna: Ruben, Gad, Asser, Sebulon, Dan och Naphthali.
14 Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
Och Leviterna skola begynna, och säga till hvar man af Israel med klara röst:
15 “La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Förbannad vare den som gör en afgud eller gjutet beläte, Herrans styggelse; ett verk, som konstnärers händer gjort hafva, och sätter det hemliga; och allt folket skall svara och säga: Amen.
16 “La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Förbannad vare den som bannar sin fader eller moder; och allt folket skall svara och säga: Amen.
17 “La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Förbannad vare den som flyttar sins nästas råmärke; och allt folket skall säga: Amen.
18 “La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Förbannad vare den som låter en blindan fara vill på vägenom; och allt folket skall säga: Amen.
19 “La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Förbannad vare den som böjer främlingens, dens faderlösas och enkones rätt; och allt folket skall säga: Amen.
20 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Förbannad vare den som ligger när sins faders hustru, att han upptäcker sins faders täckelse; och allt folket skall säga: Amen.
21 “La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Förbannad vare den som beligger någon fänad; och allt folket skall säga: Amen.
22 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da’yar’uwarsa,’yar mahaifinsa ko’yar mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Förbannad vare den som ligger när sina syster, den hans faders eller moders dotter är; och allt folket skall säga: Amen.
23 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Förbannad vare den som ligger när sina sväro; och allt folket skall säga: Amen.
24 “La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Förbannad vare den som slår sin nästa hemliga; och allt folket skall säga: Amen.
25 “La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Förbannad vare den som tager mutor, att han ens oskyldigs blods själ slå skall; och allt folket skall säga: Amen.
26 “La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Förbannad vare den som icke fullkomnar all denna lagsens ord, så att han gör derefter; och allt folket skall säga: Amen.

< Maimaitawar Shari’a 27 >