< Maimaitawar Shari’a 27 >

1 Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
I zapovjedi Mojsije sa starješinama Izrailjevijem narodu govoreæi: držite sve ove zapovijesti koje vam ja danas zapovijedam.
2 Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
I kad prijeðeš preko Jordana u zemlju koju ti daje Gospod Bog tvoj, podigni sebi kamenje veliko i namaži ga kreèem.
3 Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
I napiši na njemu sve rijeèi ovoga zakona, kad prijeðeš da uðeš u zemlju koju ti daje Gospod Bog tvoj, u zemlju gdje teèe mlijeko i med, kao što ti je kazao Gospod Bog otaca tvojih.
4 Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
Kada dakle prijeðeš preko Jordana, podigni to kamenje, za koje ti zapovijedam danas, na gori Evalu, i namaži ga kreèem.
5 Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
I naèini ondje oltar Gospodu Bogu svojemu, oltar od kamenja, ali ga nemoj gvožðem tesati.
6 Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
Od cijela kamenja naèini oltar Gospodu Bogu svojemu, i na njemu prinesi Gospodu Bogu svojemu žrtve paljenice.
7 Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
Prinesi i zahvalne žrtve, i jedi ih ondje, i veseli se pred Gospodom Bogom svojim.
8 Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
I napiši na tom kamenju sve rijeèi ovoga zakona dobro i razgovijetno.
9 Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
I reèe Mojsije i sveštenici Leviti svemu Izrailju govoreæi: pazi i èuj Izrailju, danas si postao narod Gospoda Boga svojega.
10 Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
Zato slušaj glas Gospoda Boga svojega, i tvori zapovijesti njegove i uredbe njegove, koje ti ja danas zapovijedam.
11 A wannan rana Musa ya umarce mutane,
I zapovjedi Mojsije u onaj dan narodu govoreæi:
12 Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
Ovi neka stanu da blagosiljaju narod na gori Garizinu, kad prijeðete preko Jordana: Simeun, Levije, Juda, Isahar, Josif i Venijamin.
13 Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
A ovi neka stanu da proklinju na gori Evalu: Ruvim, Gad, Asir, Zavulon, Dan i Neftalim.
14 Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
I neka progovore Leviti glasovito i reku svjema u Izrailju:
15 “La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Proklet da je èovjek koji bi naèinio lik rezan ili liven, stvar gadnu pred Gospodom, djelo ruku umjetnièkih, ako bi i na skrivenu mjestu metnuo. A sav narod odgovarajuæi neka reèe: amin.
16 “La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Proklet da je koji bi ružio oca svojega ili mater svoju. A sav narod neka reèe: amin.
17 “La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Proklet da je koji bi pomakao meðu bližnjega svojega. A sav narod neka reèe: amin.
18 “La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Proklet da je koji bi zaveo slijepca s puta. A sav narod neka reèe: amin.
19 “La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Proklet da je koji bi izvrnuo pravicu došljaku, siroti ili udovici. A sav narod neka reèe: amin.
20 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Proklet da je koji bi obležao ženu oca svojega, te otkrio skut oca svojega. A sav narod neka reèe: amin.
21 “La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Proklet da je koji bi obležao kakvo god živinèe. A sav narod neka reèe: amin.
22 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da’yar’uwarsa,’yar mahaifinsa ko’yar mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Proklet da je koji bi obležao sestru svoju, kæer oca svojega ili kæer matere svoje. A sav narod neka reèe: amin.
23 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Proklet da je koji bi obležao taštu svoju. A sav narod neka reèe: amin.
24 “La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Proklet da je koji bi ubio bližnjega svojega iz potaje. A sav narod neka reèe: amin.
25 “La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Proklet da je koji bi primio kakav poklon da ubije èovjeka prava. A sav narod neka reèe: amin.
26 “La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Proklet da je koji ne bi ostao na rijeèima ovoga zakona, i tvorio ih. A sav narod neka reèe: amin.

< Maimaitawar Shari’a 27 >