< Maimaitawar Shari’a 27 >

1 Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
Og Moses og de eldste i Israel bød folket og sa: Ta vare på alle de bud jeg gir eder idag!
2 Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
Og når I kommer over Jordan til det land Herren din Gud gir dig, da skal du reise op nogen store stener og stryke dem over med kalk.
3 Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
På dem skal du, når du er kommet over, skrive alle ordene i denne lov, forat du kan komme inn i det land Herren din Gud gir dig, et land som flyter med melk og honning, således som Herren, dine fedres Gud, har tilsagt dig.
4 Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
Så snart I er kommet over Jordan, skal I reise op disse stener som jeg idag gir eder befaling om, på Ebal-fjellet, og du skal stryke dem over med kalk.
5 Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
Og du skal bygge Herren din Gud et alter der, et alter av stener; du skal ikke bruke jern på dem.
6 Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
Av hele stener skal du bygge Herrens, din Guds alter, og du skal ofre Herren din Gud brennoffer på det.
7 Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
Og du skal ofre takkoffer og ete dem der og være glad for Herrens, din Guds åsyn.
8 Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
Og du skal skrive på stenene alle ordene i denne lov, klart og tydelig.
9 Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
Og Moses og de levittiske prester talte til hele Israel og sa: Gi akt og hør, Israel! På denne dag er du blitt Herrens, din Guds folk.
10 Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
Så lyd da Herrens, din Guds røst, og hold hans bud og hans lover, som jeg gir dig idag!
11 A wannan rana Musa ya umarce mutane,
Samme dag bød Moses folket og sa:
12 Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
Når I er kommet over Jordan, da skal disse stå på fjellet Garisim og velsigne folket: Simeon og Levi og Juda og Issakar og Josef og Benjamin.
13 Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
Og disse skal stå på fjellet Ebal og lyse forbannelse: Ruben, Gad og Aser og Sebulon, Dan og Naftali.
14 Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
Og levittene skal ta til orde og si med høi røst til hver mann i Israel:
15 “La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Forbannet være den mann som gjør et utskåret eller et støpt billede, en vederstyggelighet for Herren, et verk av en kunstners hender, og stiller det op i lønndom! Og alt folket skal svare og si: Amen.
16 “La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Forbannet være den som ringeakter sin far eller sin mor! Og alt folket skal si: Amen.
17 “La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Forbannet være den som flytter merkestenene mellem sig og sin næste! Og alt folket skal si: Amen.
18 “La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Forbannet være den som får en blind til å fare vill på veien! Og alt folket skal si: Amen.
19 “La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Forbannet være den som bøier retten for en fremmed, en farløs og en enke! Og alt folket skal si: Amen.
20 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Forbannet være den som ligger hos sin fars hustru, for han har vanæret sin fars leie! Og alt folket skal si: Amen.
21 “La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Forbannet være den som har omgang med noget dyr! Og alt folket skal si: Amen.
22 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da’yar’uwarsa,’yar mahaifinsa ko’yar mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Forbannet være den som ligger hos sin søster, sin fars eller sin mors datter! Og alt folket skal si: Amen.
23 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Forbannet være den som ligger hos sin hustrus mor! Og alt folket skal si: Amen.
24 “La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Forbannet være den som slår sin næste ihjel i lønndom! Og alt folket skal si: Amen.
25 “La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Forbannet være den som tar imot gaver for å slå nogen ihjel og utøser uskyldig blod! Og alt folket skal si: Amen.
26 “La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Forbannet være den som ikke holder ordene i denne lov og ikke gjør efter dem! Og alt folket skal si: Amen.

< Maimaitawar Shari’a 27 >