< Maimaitawar Shari’a 27 >

1 Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
Moïse et les anciens d'Israël donnèrent cet ordre au peuple: « Observez tous les commandements que je vous prescris aujourd'hui.
2 Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
Le jour où vous passerez le Jourdain pour entrer dans le pays que l'Éternel, votre Dieu, vous donne, vous dresserez de grandes pierres et vous les enduirez de plâtre.
3 Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
Tu écriras sur elles toutes les paroles de cette loi, quand tu auras passé le Jourdain, pour entrer dans le pays que l'Éternel, ton Dieu, te donne, un pays où coulent le lait et le miel, comme te l'a promis l'Éternel, le Dieu de tes pères.
4 Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
Lorsque tu auras passé le Jourdain, tu dresseras sur le mont Ebal ces pierres que je te commande aujourd'hui, et tu les enduiras de plâtre.
5 Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
Tu y bâtiras un autel à Yahvé ton Dieu, un autel de pierres. Tu n'y emploieras pas d'outil en fer.
6 Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
Tu bâtiras l'autel de Yahvé, ton Dieu, avec des pierres non taillées. Tu y offriras des holocaustes à l'Éternel, ton Dieu.
7 Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
Tu y sacrifieras des sacrifices de prospérité et tu y mangeras. Tu te réjouiras devant l'Éternel, ton Dieu.
8 Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
Tu écriras sur les pierres toutes les paroles de cette loi, très clairement. »
9 Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
Moïse et les prêtres lévitiques parlèrent à tout Israël en disant: « Tais-toi et écoute, Israël! Aujourd'hui, tu es devenu le peuple de l'Éternel, ton Dieu.
10 Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
Tu obéiras donc à la voix de Yahvé ton Dieu, et tu mettras en pratique ses commandements et ses lois, que je te prescris aujourd'hui. »
11 A wannan rana Musa ya umarce mutane,
Le même jour, Moïse donna cet ordre au peuple:
12 Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
« Voici ceux qui se tiendront sur le mont Garizim pour bénir le peuple, lorsque vous aurez franchi le Jourdain: Siméon, Lévi, Juda, Issacar, Joseph et Benjamin.
13 Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
Ceux-là se tiendront sur le mont Ebal pour la malédiction: Ruben, Gad, Aser, Zabulon, Dan et Nephtali.
14 Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
Les Lévites diront d'une voix forte à tous les hommes d'Israël:
15 “La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
« Maudit est l'homme qui fait une image gravée ou fondue, une abomination pour Yahvé, l'œuvre des mains de l'artisan, et qui la place dans le secret ». Tout le peuple répondra et dira: « Amen.
16 “La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
« Maudit soit celui qui déshonore son père ou sa mère ». Tout le peuple dira « Amen ».
17 “La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
« Maudit soit celui qui enlève le repère de son prochain ». Tout le peuple dira « Amen ».
18 “La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
« Maudit soit celui qui égare l'aveugle sur la route ». Tout le peuple dira « Amen ».
19 “La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
« Maudit soit celui qui refuse de rendre justice à l'étranger, à l'orphelin et à la veuve ». Tout le peuple dira « Amen ».
20 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
« Maudit soit celui qui couche avec la femme de son père, car il déshonore la couche de son père ». Tout le peuple dira « Amen ».
21 “La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
« Maudit soit celui qui couche avec n'importe quelle espèce d'animal ». Tout le peuple dira « Amen ».
22 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da’yar’uwarsa,’yar mahaifinsa ko’yar mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
« Maudit soit celui qui couche avec sa sœur, la fille de son père ou la fille de sa mère ». Tout le peuple dira « Amen ».
23 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
« Maudit soit celui qui couche avec sa belle-mère ». Tout le peuple dira « Amen ».
24 “La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
« Maudit soit celui qui tue secrètement son prochain ». Tout le peuple dira « Amen ».
25 “La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
« Maudit soit celui qui accepte un pot-de-vin pour tuer un innocent ». Tout le peuple dira « Amen ».
26 “La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
« Maudit soit celui qui ne respecte pas les paroles de cette loi en les mettant en pratique. Tout le peuple dira 'Amen'. »

< Maimaitawar Shari’a 27 >