< Maimaitawar Shari’a 27 >
1 Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
Then Moses with the Elders of Israel commanded the people, saying, Keepe all the comandements, which I command you this day.
2 Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
And when ye shall passe ouer Iorden vnto the lande which the Lord thy God giueth thee, thou shalt set thee vp great stones, and playster them with plaister,
3 Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
And shalt write vpon them all the words of this Lawe, when thou shalt come ouer, that thou mayest go into the land which the Lord thy God giueth thee: a land that floweth with milke and hony, as the Lord God of thy fathers hath promised thee.
4 Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
Therefore when ye shall passe ouer Iorden, ye shall set vp these stones, which I command you this daye in mount Ebal, and thou shalt plaister them with plaister.
5 Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
And there shalt thou build vnto the Lord thy God an altar, euen an altar of stones: thou shalt lift none yron instrument vpon them.
6 Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
Thou shalt make the altar of the Lord thy God of whole stones, and offer burnt offerings thereon vnto the Lord thy God.
7 Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
And thou shalt offer peace offrings, and shalt eate there and reioyce before the Lord thy God:
8 Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
And thou shalt write vpon the stones al the words of this Law, well and plainely.
9 Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
And Moses and the Priestes of the Leuites spake vnto all Israel, saying, Take heede and heare, O Israel: this day thou art become the people of the Lord thy God.
10 Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
Thou shalt hearken therefore vnto the voyce of the Lord thy God, and do his commandements and his ordinances, which I commande thee this day.
11 A wannan rana Musa ya umarce mutane,
And Moses charged the people the same day, saying,
12 Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
These shall stand vpon mount Gerizzim, to blesse the people when ye shall passe ouer Iorden: Simeon, and Leui, and Iudah, and Issachar, and Ioseph, and Beniamin.
13 Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
And these shall stand vpon mount Ebal to curse: Reuben, Gad, and Asher, and Zebulun, Dan, and Naphtali.
14 Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
And the Leuites shall answere and say vnto all the men of Israel with a loude voyce,
15 “La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be the man that shall make any carued or molten image, which is an abomination vnto the Lord, the worke of the hands of the craftesman, and putteth it in a secrete place: And all the people shall answere, and say: So be it.
16 “La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he that curseth his father and his mother: And all the people shall say: So be it.
17 “La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he that remoueth his neighbors marke: And all the people shall say: So be it.
18 “La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he that maketh ye blinde go out of the way: And all the people shall say: So be it.
19 “La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he that hindreth the right of the stranger, the fatherles, and the widow: And all the people shall say: So be it.
20 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be hee that lyeth with his fathers wife: for he hath vncouered his fathers skirt: And all the people shall say: So be it.
21 “La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he that lieth with any beast: And all the people shall say: So be it.
22 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da’yar’uwarsa,’yar mahaifinsa ko’yar mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he that lyeth with his sister, the daughter of his father, or the daughter of his mother: And all the people shall say: So be it.
23 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he that lyeth with his mother in law: And all the people shall say: So be it.
24 “La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be hee that smiteth his neyghbour secretly: And all the people shall say: So be it.
25 “La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he that taketh a reward to put to death innocent blood: And all the people shall say: So be it.
26 “La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he that confirmeth not all the wordes of this Law, to do them: And all the people shall say: So be it.