< Maimaitawar Shari’a 27 >

1 Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
Then Moses and the responsible men of Israel gave the people these orders: Keep all the orders which I have given you this day;
2 Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
And on the day when you go over Jordan into the land which the Lord your God is giving you, put up great stones, coating them with building-paste,
3 Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
And writing on them all the words of this law, after you have gone over; so that you may take the heritage which the Lord your God is giving you, a land flowing with milk and honey, as the Lord, the God of your fathers, has said.
4 Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
And when you have gone over Jordan, you are to put up these stones, as I have said to you today, in Mount Ebal, and have them coated with building-paste.
5 Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
There you are to make an altar to the Lord your God, of stones on which no iron instrument has been used.
6 Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
You are to make the altar of the Lord your God of uncut stones; offering on it burned offerings to the Lord your God:
7 Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
And you are to make your peace-offerings, feasting there with joy before the Lord your God.
8 Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
And put on the stones all the words of this law, writing them very clearly.
9 Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
Then Moses and the priests, the Levites, said to all Israel, Be quiet and give ear, O Israel; today you have become the people of the Lord your God.
10 Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
For this cause you are to give ear to the voice of the Lord your God, and do his orders and his laws which I give you this day.
11 A wannan rana Musa ya umarce mutane,
That same day Moses said to the people,
12 Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
These are to take their places on Mount Gerizim for blessing the people when you have gone over Jordan: Simeon and Levi and Judah and Issachar and Joseph and Benjamin;
13 Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
And these are to be on Mount Ebal for the curse: Reuben, Gad, and Asher, and Zebulun, Dan, and Naphtali.
14 Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
Then the Levites are to say in a loud voice to all the men of Israel,
15 “La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed is the man who makes any image of wood or stone or metal, disgusting to the Lord, the work of man's hands, and puts it up in secret. And let all the people say, So be it.
16 “La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed is he who does not give honour to his father or mother. And let all the people say, So be it.
17 “La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed is he who takes his neighbour's landmark from its place. And let all the people say, So be it.
18 “La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed is he by whom the blind are turned out of the way. And let all the people say, So be it.
19 “La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed is he who gives a wrong decision in the cause of a man from a strange land, or of one without a father, or of a widow. And let all the people say, So be it.
20 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed is he who has sex relations with his father's wife, for he has put shame on his father. And let all the people say, So be it.
21 “La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed is he who has sex relations with any sort of beast. And let all the people say, So be it.
22 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da’yar’uwarsa,’yar mahaifinsa ko’yar mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed is he who has sex relations with his sister, the daughter of his father or of his mother. And let all the people say, So be it.
23 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed is he who has sex relations with his mother-in-law. And let all the people say, So be it.
24 “La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed is he who takes his neighbour's life secretly. And let all the people say, So be it.
25 “La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed is he who for a reward puts to death one who has done no wrong. And let all the people say, So be it.
26 “La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed is he who does not take this law to heart to do it. And let all the people say, So be it.

< Maimaitawar Shari’a 27 >