< Maimaitawar Shari’a 27 >
1 Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
And Moses and the elders of Israel commanded the people, saying, Keep all the commandment which I command you this day.
2 Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
And it shall be on the day when ye shall pass over the Jordan to the land which Jehovah thy God gives thee, that thou shall set up for thee great stones, and plaster them with plaster.
3 Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
And thou shall write upon them all the words of this law when thou have passed over, that thou may go in to the land which Jehovah thy God gives thee, a land flowing with milk and honey, as Jehovah, the God of thy fathers, has promised thee.
4 Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
And it shall be, when ye have passed over the Jordan, that ye shall set up these stones, which I command you this day, in mount Ebal, and thou shall plaster them with plaster.
5 Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
And there thou shall build an altar to Jehovah thy God, an altar of stones. Thou shall lift up no iron upon them.
6 Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
Thou shall build the altar of Jehovah thy God of unhewn stones. And thou shall offer burnt offerings on it to Jehovah thy God.
7 Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
And thou shall sacrifice peace offerings, and shall eat there, and thou shall rejoice before Jehovah thy God.
8 Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
And thou shall write upon the stones all the words of this law very plainly.
9 Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
And Moses and the priests the Levites spoke to all Israel, saying, Keep silence, and hearken, O Israel. This day thou have become the people of Jehovah thy God.
10 Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
Thou shall therefore obey the voice of Jehovah thy God, and do his commandments and his statutes, which I command thee this day.
11 A wannan rana Musa ya umarce mutane,
And Moses charged the people the same day, saying,
12 Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
These shall stand upon mount Gerizim to bless the people, when ye have passed over the Jordan: Simeon, and Levi, and Judah, and Issachar, and Joseph, and Benjamin.
13 Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
And these shall stand upon mount Ebal for the curse: Reuben, Gad, and Asher, and Zebulun, Dan, and Naphtali.
14 Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
And the Levites shall answer, and say to all the men of Israel with a loud voice,
15 “La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be the man who makes a graven or molten image, an abomination to Jehovah, the work of the hands of the craftsman, and sets it up in secret. And all the people shall answer and say, Truly.
16 “La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he who dishonors his father or his mother. And all the people shall say, Truly.
17 “La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he who removes his neighbor's landmark. And all the people shall say, Truly.
18 “La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he who makes the blind to wander out of the way. And all the people shall say, Truly.
19 “La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he who distorts the justice to the sojourner, fatherless, and widow. And all the people shall say, Truly.
20 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he who lies with his father's wife, because he has uncovered his father's skirt. And all the people shall say, Truly.
21 “La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he who lies with any manner of beast. And all the people shall say, Truly.
22 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da’yar’uwarsa,’yar mahaifinsa ko’yar mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he who lies with his sister, the daughter of his father, or the daughter of his mother. And all the people shall say, Truly.
23 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he who lies with his mother-in-law. And all the people shall say, Truly.
24 “La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he who smites his neighbor in secret. And all the people shall say, Truly.
25 “La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed be he who takes a bribe to kill an innocent man. And all the people shall say, Truly.
26 “La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Cursed is every man who does not continue in all the words of this law to do them. And all the people shall say, Truly.