< Maimaitawar Shari’a 27 >

1 Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
Musa kod jodong Israel duto ne ochiko oganda niya, “Rituru chikegi ma amiyou kawuono
2 Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
Ka usengʼado aora Jordan ma uchopo e piny ma Jehova Nyasaye ma Nyasachu miyou, keturu kite moko kendo uwirgi maber.
3 Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
Ndikuru kuomgi weche duto manie chike ka usengʼado ma uchopo e piny ma Jehova Nyasaye ma Nyasachu miyou ma en piny mopongʼ gi chak kod mor kich, mana kaka Jehova Nyasaye ma Nyasach kwereu nosingonu.
4 Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
Ka usengʼado aora Jordan, chunguru kitegi e Got Ebal mana kaka achikou kawuono ka uwirogi maber.
5 Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
Geruru kendo mar misango ne Jehova Nyasaye ma Nyasachu, ma en kendo mar misango molos gi kite. Kitego kik paa gi chuma.
6 Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
Geruru kendo mar misango mar Jehova Nyasaye ma Nyasachu gi kite ma ok opa, kendo utim misango miwangʼo pep kanyo ne Jehova Nyasaye ma Nyasachu.
7 Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
Timuru misengini mag lalruok kanyo, ka uchiemo kendo ubedo gi mor e nyim Jehova Nyasaye ma Nyasachu.
8 Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
Kendo ndikuru weche duto mag chikni mochanore e kite ma usechungono.”
9 Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
Eka Musa kod jodolo ma gin jo-Lawi nowachone jo-Israel duto niya, “Lingʼuru, yaye Israel, bende chikuru itu! Koro usebedo jo-Jehova Nyasaye ma Nyasachu.
10 Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
Luor Jehova Nyasaye ma Nyasachi kendo mondo iluw chikene kod buchene ma amiyi kawuono.”
11 A wannan rana Musa ya umarce mutane,
E odiechiengʼ onogono Musa nochiko oganda kowachonegi niya,
12 Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
Ka usengʼado aora Jordan, to dhoudigi nobi e Got Gerizim mondo gigwedh ji: Simeon, Lawi, Juda, Isakar, Josef kod Benjamin.
13 Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
Kendo dhoudigi nochungʼ e Got Ebal ka gihulo weche mag kwongʼ: Reuben, Gad, Asher, Zebulun, Dan kod Naftali.
14 Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
Jo-Lawi biro somone jo-Israel gi dwol maduongʼ niya,
15 “La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
“Okwongʼ ngʼat moloso kido milamo, kata nyiseche mopa, ma en gima mono e nyim Jehova Nyasaye, tij lwedo mar japecho kendo mochungi kama opondo.” Eka ji duto nodwok niya, “Amin!”
16 “La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
“Okwongʼ ngʼat ma ok oluoro wuon kata min.” Eka ji duto nodwok niya, “Amin!”
17 “La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
“Okwongʼ ngʼat masudo tongʼ mar jakiepe.” Eka ji duto nodwok niya, “Amin!”
18 “La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
“Okwongʼ ngʼat ma wito muofu e yo.” Eka ji duto nodwok niya, “Amin!”
19 “La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
“Okwongʼ ngʼat maketho buch japiny moro, nyathi kich kod dhako ma chwore otho.” Eka ji duto nodwok niya, “Amin!”
20 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
“Okwongʼ ngʼat ma terore gi chi wuon, nimar odwanyo kitanda wuon.” Eka ji duto nodwok niya, “Amin!”
21 “La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
“Okwongʼ ngʼat ma oterore gi chiayo.” Eka ji duto nodwok niya, “Amin!”
22 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da’yar’uwarsa,’yar mahaifinsa ko’yar mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
“Okwongʼ ngʼat ma terore gi nyamin kata nyar wuon kata nyar min mare.” Eka ji duto nodwok niya, “Amin!”
23 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
“Okwongʼ ngʼat ma oterore gi mar-mare.” Eka ji duto nodwok niya, “Amin!”
24 “La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
“Okwongʼ ngʼat ma onego nyawadgi lingʼ-lingʼ.” Eka ji duto nodwok niya, “Amin!”
25 “La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
“Okwongʼ ngʼat ma okawo asoya mondo oneg ngʼat maonge ketho.” Eka ji duto nodwok niya, “Amin!”
26 “La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
“Okwongʼ ngʼat ma ok orito weche mag chikni kata luwogi ka ojiwogi.” Eka ji duto nodwok niya, “Amin!”

< Maimaitawar Shari’a 27 >