< Maimaitawar Shari’a 26 >
1 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta,
“And it has been, when you come into the land which your God YHWH is giving to you [for] an inheritance, and you have possessed it and dwelt in it,
2 sai ku ɗauki’ya’yan fari na dukan amfanin gonar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku zuba a kwando. Sa’an nan ku je wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă zama mazauni don Sunansa,
that you have taken from the first of all the fruits of the ground, which you bring in out of your land which your God YHWH is giving to you, and have put [it] in a basket, and gone to the place which your God YHWH chooses to cause His Name to dwell there.
3 ku faɗa wa firist da yake aiki a lokacin, “Na sakankance yau ga Ubangiji Allahnka, cewa na zo ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninmu.”
And you have come to the priest who is in those days, and have said to him, I have declared to your God YHWH today that I have come into the land which YHWH has sworn to our fathers to give to us;
4 Firist ɗin zai karɓi kwandon daga hannuwanku yă sa shi a ƙasa a gaban bagaden Ubangiji Allahnku.
and the priest has taken the basket out of your hand and placed it before the altar of your God YHWH.
5 Sa’an nan za ku furta a gaban Ubangiji Allahnku cewa, “Mahaifina mutumin Aram ne mai yawo, ya gangara zuwa Masar da mutane kaɗan, ya zauna a can, ya kuma zama babban al’umma, mai iko da kuma mai yawa.
And you have answered and said before your God YHWH, My father [is] a perishing Aramean! And he goes down to Egypt, and sojourns there with few men, and becomes a great, mighty, and populous nation there;
6 Amma Masarawa suka wulaƙanta mu suka sa muka sha wahala, suna sa mu aikin dole.
and the Egyptians do us evil, and afflict us, and put hard service on us;
7 Sai muka yi kuka ga Ubangiji Allahn kakanninmu, Ubangiji kuwa ya ji kukanmu, ya kuma azabar da muke sha, da wahalar da muke sha, da danniyar da suke yin mana.
and we cry to YHWH, God of our fathers, and YHWH hears our voice, and sees our affliction, and our labor, and our oppression;
8 Sai Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu mai ƙarfi da kuma iko, da razana mai girma da kuma alamu banmamaki da al’ajabai.
and YHWH brings us out from Egypt by a strong hand, and by an outstretched arm, and by great fear, and by signs, and by wonders,
9 Ya kawo mu wannan wuri, ya kuma ba mu wannan ƙasa, ƙasa mai zub da madara da kuma zuma;
and He brings us to this place, and gives this land to us—a land flowing with milk and honey.
10 yanzu kuwa na kawo’ya’yan fari na gonar da kai, ya Ubangiji ka ba ni.” Sai ku sa kwandon a gaban Ubangiji Allahnku, sa’an nan ku rusuna a gabansa.
And now, behold, I have brought in the first of the fruits of the ground which you have given to me, O YHWH. (And you have placed it before your God YHWH, and bowed yourself before your God YHWH,
11 Ku da Lawiyawa da baƙin da suke a cikinku, za ku yi murna cikin dukan abubuwa masu kyau da Ubangiji Allahnku ya ba ku tare da gidanku.
and rejoiced in all the good which your God YHWH has given to you and to your house—you, and the Levite, and the sojourner who [is] in your midst.)
12 Sa’ad da kuka gama fitar da kashi ɗaya bisa goma na dukan amfanin gona a shekara ta uku, shekarar zakka, za ku ba da su ga Balawe, baƙo, maraya da kuma gwauruwa, don su ci a cikin garuruwanku su ƙoshi.
When you complete to tithe all the tithe of your increase in the third year, the year of the tithe, then you have given to the Levite, to the sojourner, to the fatherless, and to the widow, and they have eaten within your gates and been satisfied,
13 Sa’an nan ku faɗa wa Ubangiji Allahnku, “Na cire tsattsarkan rabo daga gidana na kuma ba wa Balawe, baƙo, maraya da gwauruwa, bisa ga dukan abin da ka umarta. Ban ja gefe daga umarnanka ko in manta da wani a cikinsu ba.
and you have said before your God YHWH, I have put away the separated thing out of the house, and have also given it to the Levite, and to the sojourner, and to the orphan, and to the widow, according to all Your command which You have commanded me; I have not passed over from Your commands, nor have I forgotten.
14 Ban ci wani daga cikin tsattsarkan rabo yayinda nake makoki, ko in cire wani rabo mai tsarki yayinda nake marar tsarki, ko in miƙa wani sashensa ga matattu ba. Na yi biyayya ga Ubangiji Allahna, na aikata kome da ka umarce ni.
I have not eaten of it in my affliction, nor have I put away of it for uncleanness, nor have I given of it for the dead; I have listened to the voice of my God YHWH; I have done according to all that You have commanded me;
15 Ka duba ƙasa daga sama, mazauninka mai tsarki, ka albarkace mutanenka Isra’ila da kuma ƙasar da ka ba mu kamar yadda ka yi wa kakanninmu alkawari da rantsuwa, ƙasa mai zub da madara da zuma.”
look from Your holy habitation, from the heavens, and bless Your people Israel and the ground which You have given to us, as You have sworn to our fathers—a land flowing [with] milk and honey.
16 Yau Ubangiji Allahnku ya umarce ku ku bi waɗannan ƙa’idodi da kuma dokoki, cikin natsuwa ku kiyaye su da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
This day your God YHWH is commanding you to do these statutes and judgments; and you have listened and done them with all your heart and with all your soul.
17 Kun furta a wannan rana cewa Ubangiji shi ne Allahnku, cewa za ku kuma yi tafiya a hanyoyinsa, cewa za ku kiyaye ƙa’idodinsa, umarnansa da kuma dokokinsa, kuka kuma ce za ku yi masa biyayya.
Today you have proclaimed YHWH to be to you for God, that [you are] to walk in His ways, and to keep His statutes, and His commands, and His judgments, and to listen to His voice.
18 Ubangiji kuwa ya furta a wannan rana cewa ku mutanensa ne, mallakarsa kamar yadda ya yi alkawari, da kuma cewa za ku kiyaye dukan umarnansa.
And today YHWH has proclaimed you to be to Him for a people, a peculiar treasure, as He has spoken to you, that [you are] to keep all His commands,
19 Ya furta cewa zai sa ku zama masu yabo, masu suna, masu daraja, fiye da dukan al’umman da ya yi. Za ku zama jama’a tsattsarka ta Ubangiji Allahnku, kamar yadda ya yi alkawari.
so as to make you highest above all the nations whom He has made for a praise, and for a name, and for beauty, and for your being a holy people to your God YHWH, as He has spoken.”