< Maimaitawar Shari’a 26 >

1 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta,
And it shall come to pass, when thou art come in unto the land which the Lord thy God giveth thee for an inheritance, and thou hast taken possession of it, and dwellest therein:
2 sai ku ɗauki’ya’yan fari na dukan amfanin gonar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku zuba a kwando. Sa’an nan ku je wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă zama mazauni don Sunansa,
That thou shalt take of the first of all the fruit of the soil, which thou shalt bring in from thy land which the Lord thy God giveth thee, and shalt put it in a basket; and thou shalt go unto the place which the Lord thy God will choose to let his name dwell there.
3 ku faɗa wa firist da yake aiki a lokacin, “Na sakankance yau ga Ubangiji Allahnka, cewa na zo ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninmu.”
And thou shalt come unto the priest that may be in those days, and thou shalt say unto him, I give thanks this day unto the Lord thy God, that I am come into the land which the Lord swore unto our fathers to give to us.
4 Firist ɗin zai karɓi kwandon daga hannuwanku yă sa shi a ƙasa a gaban bagaden Ubangiji Allahnku.
And the priest shall take the basket out of thy hand, and set it down before the altar of the Lord thy God.
5 Sa’an nan za ku furta a gaban Ubangiji Allahnku cewa, “Mahaifina mutumin Aram ne mai yawo, ya gangara zuwa Masar da mutane kaɗan, ya zauna a can, ya kuma zama babban al’umma, mai iko da kuma mai yawa.
And thou shalt commence and say before the Lord thy God, A Syrian, wandering about, was my father, and he went down into Egypt, and sojourned there with a family few in number, and he became there a nation, great, mighty, and numerous.
6 Amma Masarawa suka wulaƙanta mu suka sa muka sha wahala, suna sa mu aikin dole.
And the Egyptians treated us ill, and afflicted us, and laid upon us hard labor;
7 Sai muka yi kuka ga Ubangiji Allahn kakanninmu, Ubangiji kuwa ya ji kukanmu, ya kuma azabar da muke sha, da wahalar da muke sha, da danniyar da suke yin mana.
And then we cried unto the Eternal, the God of our fathers; and the Lord heard our voice, and looked on our affliction, and our trouble, and our oppression;
8 Sai Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu mai ƙarfi da kuma iko, da razana mai girma da kuma alamu banmamaki da al’ajabai.
And the Lord brought us forth out of Egypt with a mighty hand, and with an outstretched arm, and with great terror, and with signs, and with wonders;
9 Ya kawo mu wannan wuri, ya kuma ba mu wannan ƙasa, ƙasa mai zub da madara da kuma zuma;
And he brought us unto this place, and gave unto us this land, a land flowing with milk and honey.
10 yanzu kuwa na kawo’ya’yan fari na gonar da kai, ya Ubangiji ka ba ni.” Sai ku sa kwandon a gaban Ubangiji Allahnku, sa’an nan ku rusuna a gabansa.
And now, behold, I have brought the first of the fruits of the soil, which thou hast given me, O Lord; and thou shalt set it down before the Lord thy God, and prostrate thyself before the Lord thy God;
11 Ku da Lawiyawa da baƙin da suke a cikinku, za ku yi murna cikin dukan abubuwa masu kyau da Ubangiji Allahnku ya ba ku tare da gidanku.
And thou shalt rejoice with every good thing which the Lord thy God hath given unto thee, and unto thy house, thou, with the Levite, and the stranger that is in the midst of thee.
12 Sa’ad da kuka gama fitar da kashi ɗaya bisa goma na dukan amfanin gona a shekara ta uku, shekarar zakka, za ku ba da su ga Balawe, baƙo, maraya da kuma gwauruwa, don su ci a cikin garuruwanku su ƙoshi.
When thou hast made an end of giving away all the tithe of thy produce in the third year, the year of the tithing, and hast given it unto the Levite, to the stranger, to the fatherless, and to the widow, and they have eaten it within thy gates, and are satisfied:
13 Sa’an nan ku faɗa wa Ubangiji Allahnku, “Na cire tsattsarkan rabo daga gidana na kuma ba wa Balawe, baƙo, maraya da gwauruwa, bisa ga dukan abin da ka umarta. Ban ja gefe daga umarnanka ko in manta da wani a cikinsu ba.
Then shalt thou say before the Lord thy God, I have removed away the hallowed things out of the house, and I have also given them unto the Levite, and unto the stranger, to the fatherless, and to the widow, according to all thy commandment which thou hast commanded me; I have not deviated from thy commandments, and I have not forgotten;
14 Ban ci wani daga cikin tsattsarkan rabo yayinda nake makoki, ko in cire wani rabo mai tsarki yayinda nake marar tsarki, ko in miƙa wani sashensa ga matattu ba. Na yi biyayya ga Ubangiji Allahna, na aikata kome da ka umarce ni.
I have not eaten thereof in my mourning, neither have I removed away aught thereof in an unclean state, nor have I given aught thereof for the dead: I have hearkened to the voice of the Lord my God, I have done all, just as thou hast commanded me.
15 Ka duba ƙasa daga sama, mazauninka mai tsarki, ka albarkace mutanenka Isra’ila da kuma ƙasar da ka ba mu kamar yadda ka yi wa kakanninmu alkawari da rantsuwa, ƙasa mai zub da madara da zuma.”
Look down from the habitation of thy holiness, from the heavens, and bless thy people Israel, and the soil which thou hast given unto us, as thou hast sworn unto our fathers, a land flowing with milk and honey.
16 Yau Ubangiji Allahnku ya umarce ku ku bi waɗannan ƙa’idodi da kuma dokoki, cikin natsuwa ku kiyaye su da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
This day the Lord thy God commandeth thee to do these statutes and ordinances; and thou shalt keep and do them with all thy heart, and with all thy soul.
17 Kun furta a wannan rana cewa Ubangiji shi ne Allahnku, cewa za ku kuma yi tafiya a hanyoyinsa, cewa za ku kiyaye ƙa’idodinsa, umarnansa da kuma dokokinsa, kuka kuma ce za ku yi masa biyayya.
Thou hast this day acknowledged the Lord, that he is thy God, and that thou wilt walk in his ways, and keep his statutes, and his commandments, and his ordinances, and hearken unto his voice;
18 Ubangiji kuwa ya furta a wannan rana cewa ku mutanensa ne, mallakarsa kamar yadda ya yi alkawari, da kuma cewa za ku kiyaye dukan umarnansa.
And the Lord hath acknowledged thee this day, that thou art unto him a peculiar people, as he hath spoken unto thee, and that thou shouldst keep all his commandments;
19 Ya furta cewa zai sa ku zama masu yabo, masu suna, masu daraja, fiye da dukan al’umman da ya yi. Za ku zama jama’a tsattsarka ta Ubangiji Allahnku, kamar yadda ya yi alkawari.
So that he may set thee highest above all nations that he hath made, in praise, and in name, and in honor; and that thou mayest be a holy people unto the Lord thy God, as he hath spoken.

< Maimaitawar Shari’a 26 >