< Maimaitawar Shari’a 26 >
1 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta,
Kad stigneš u zemlju koju ti Jahve, Bog tvoj, daje u baštinu, kad je zaposjedneš i u njoj se nastaniš,
2 sai ku ɗauki’ya’yan fari na dukan amfanin gonar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku zuba a kwando. Sa’an nan ku je wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă zama mazauni don Sunansa,
uzmi nešto prvina od svakoga ploda što ga budeš dobivao od zemlje koju ti Jahve, Bog tvoj, daje: stavi ih u košaru, otiđi u mjesto što ga Jahve, Bog tvoj, odabere da u njemu nastani svoje ime.
3 ku faɗa wa firist da yake aiki a lokacin, “Na sakankance yau ga Ubangiji Allahnka, cewa na zo ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninmu.”
Stupi k svećeniku koji bude tada vršio službu i reci: 'Priznajem danas pred Jahvom, Bogom svojim, da sam stigao u zemlju za koju se Jahve zakleo našim ocima da će je nama dati.'
4 Firist ɗin zai karɓi kwandon daga hannuwanku yă sa shi a ƙasa a gaban bagaden Ubangiji Allahnku.
Zatim će svećenik uzeti iz tvoje ruke košaru i položiti je pred žrtvenik Jahve, Boga tvoga.
5 Sa’an nan za ku furta a gaban Ubangiji Allahnku cewa, “Mahaifina mutumin Aram ne mai yawo, ya gangara zuwa Masar da mutane kaɗan, ya zauna a can, ya kuma zama babban al’umma, mai iko da kuma mai yawa.
Ti onda nastavi i reci pred Jahvom, Bogom svojim: 'Moj je otac bio aramejski lutalac koji je sa malo čeljadi sišao u Egipat da se skloni. Ali je ondje postao velikim, brojnim i moćnim narodom.
6 Amma Masarawa suka wulaƙanta mu suka sa muka sha wahala, suna sa mu aikin dole.
Egipćani su s nama postupali loše; tlačili su nas i nametnuli nam teško ropstvo.
7 Sai muka yi kuka ga Ubangiji Allahn kakanninmu, Ubangiji kuwa ya ji kukanmu, ya kuma azabar da muke sha, da wahalar da muke sha, da danniyar da suke yin mana.
Vapili smo Jahvi, Bogu otaca svojih. Jahve je čuo vapaj naš; vidje naš jad, našu nevolju i našu muku.
8 Sai Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu mai ƙarfi da kuma iko, da razana mai girma da kuma alamu banmamaki da al’ajabai.
Iz Egipta nas izvede Jahve moćnom rukom i ispruženom mišicom, velikom strahotom, znakovima i čudesima.
9 Ya kawo mu wannan wuri, ya kuma ba mu wannan ƙasa, ƙasa mai zub da madara da kuma zuma;
I dovede nas na ovo mjesto i dade nam ovu zemlju, zemlju kojom teče med i mlijeko.
10 yanzu kuwa na kawo’ya’yan fari na gonar da kai, ya Ubangiji ka ba ni.” Sai ku sa kwandon a gaban Ubangiji Allahnku, sa’an nan ku rusuna a gabansa.
I sad, evo, donosim prvine plodova sa tla što si mi ga, Jahve, dao.' Stavi ih pred Jahvu, Boga svoga, i pred Jahvom, Bogom svojim, duboko se nakloni.
11 Ku da Lawiyawa da baƙin da suke a cikinku, za ku yi murna cikin dukan abubuwa masu kyau da Ubangiji Allahnku ya ba ku tare da gidanku.
A onda zajedno s levitom i došljakom koji bude kod tebe uživaj sva dobra kojima je Jahve, Bog tvoj, obasuo tebe i dom tvoj.
12 Sa’ad da kuka gama fitar da kashi ɗaya bisa goma na dukan amfanin gona a shekara ta uku, shekarar zakka, za ku ba da su ga Balawe, baƙo, maraya da kuma gwauruwa, don su ci a cikin garuruwanku su ƙoshi.
A kad treće godine - godine desetine - završiš odjeljivanje sve desetine od svoga prihoda i dadeš levitu, došljaku, siroti i udovici po tvojim gradovima da jedu do sitosti,
13 Sa’an nan ku faɗa wa Ubangiji Allahnku, “Na cire tsattsarkan rabo daga gidana na kuma ba wa Balawe, baƙo, maraya da gwauruwa, bisa ga dukan abin da ka umarta. Ban ja gefe daga umarnanka ko in manta da wani a cikinsu ba.
tada pred Jahvom, Bogom svojim, izjavi: 'Iz kuće sam uklonio ono što je bilo posvećeno. Dao sam još i levitu, došljaku, siroti i udovici, prema svim tvojim zapovijedima koje si mi izdao. Ni jedne tvoje zapovijedi nisam prekršio ni zaboravio.
14 Ban ci wani daga cikin tsattsarkan rabo yayinda nake makoki, ko in cire wani rabo mai tsarki yayinda nake marar tsarki, ko in miƙa wani sashensa ga matattu ba. Na yi biyayya ga Ubangiji Allahna, na aikata kome da ka umarce ni.
Od toga nisam ništa jeo u žalosti; od toga nisam ništa žrtvovao u nečistoći, niti sam od toga što dao mrtvacu; slušao sam glas Jahve, Boga svoga; u svemu sam učinio kako si mi naredio.
15 Ka duba ƙasa daga sama, mazauninka mai tsarki, ka albarkace mutanenka Isra’ila da kuma ƙasar da ka ba mu kamar yadda ka yi wa kakanninmu alkawari da rantsuwa, ƙasa mai zub da madara da zuma.”
Pogledaj s nebesa, iz svoga svetog prebivališta, i blagoslovi narod svoj izraelski i zemlju koju si nam dao, zemlju kojom teče med i mlijeko - kako si se zakleo ocima našim.'
16 Yau Ubangiji Allahnku ya umarce ku ku bi waɗannan ƙa’idodi da kuma dokoki, cikin natsuwa ku kiyaye su da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
Jahve, Bog tvoj, naređuje ti danas da vršiš ove zakone i uredbe. Drži ih, dakle, i vrši svim srcem svojim i svom dušom svojom.
17 Kun furta a wannan rana cewa Ubangiji shi ne Allahnku, cewa za ku kuma yi tafiya a hanyoyinsa, cewa za ku kiyaye ƙa’idodinsa, umarnansa da kuma dokokinsa, kuka kuma ce za ku yi masa biyayya.
Danas si ugovorio s Jahvom da će ti on biti Bog, a ti da ćeš ići njegovim putovima, držati njegove zakone, njegove zapovijedi i njegove uredbe i slušati njegov glas.
18 Ubangiji kuwa ya furta a wannan rana cewa ku mutanensa ne, mallakarsa kamar yadda ya yi alkawari, da kuma cewa za ku kiyaye dukan umarnansa.
Danas je Jahve ugovorio s tobom da ćeš ti biti njegov narod, njegova predraga svojina, kako ti je obećao, i da ćeš držati sve njegove zapovijedi.
19 Ya furta cewa zai sa ku zama masu yabo, masu suna, masu daraja, fiye da dukan al’umman da ya yi. Za ku zama jama’a tsattsarka ta Ubangiji Allahnku, kamar yadda ya yi alkawari.
On će te uzvisiti čašću, imenom i slavom nad sve narode koje je stvorio; i ti ćeš biti narod posvećen Jahvi, Bogu svome, kako ti je rekao.”