< Maimaitawar Shari’a 25 >

1 Idan mūsu ya tashi tsakanin mutum biyu har abin ya kai su kotu, alƙalai kuwa suka yanke hukunci a kan batun, suka kuɓutar da marar laifi sa’an nan suka hukunta mai laifi,
S'il y a une controverse entre des hommes, qu'ils viennent en jugement et que les juges les jugent, ils justifieront le juste et condamneront le méchant.
2 in mai laifin ya cancanci bulala, alƙali zai sa yă kwanta a yi masa bulala a gabansa da yawan bulalan da ya dace da laifin,
Si le méchant est digne d'être battu, le juge le fera coucher et sera battu devant lui, selon sa méchanceté, par nombre de coups.
3 amma kada yă yi masa bulala fiye da arba’in. In ya yi masa fiye da haka, za a ƙasƙantar da ɗan’uwanku, zai kuma zama rainanne a idonku.
Il pourra le condamner à quarante coups de bâton au plus. Il n'en donnera pas davantage, de peur que, s'il en donne davantage et le batte plus que ce nombre de coups, ton frère ne soit dégradé à tes yeux.
4 Kada ku yi wa saniya takunkumi sa’ad da take tattaka hatsi.
Tu ne muselleras pas le bœuf quand il foule le grain.
5 In’yan’uwa suna zama tare, in ɗayansu ya mutu babu ɗa, kada gwauruwar tă yi aure waje da iyalin. Ɗan’uwan mijinta zai ɗauke ta, yă aure ta, yă kuma cika abin da yă kamaci ɗan’uwan miji yă yi.
Si des frères habitent ensemble, et que l'un d'eux meure et n'ait pas de fils, la femme du défunt ne sera pas mariée en dehors à un étranger. Le frère de son mari entrera chez elle, la prendra pour femme, et exercera à son égard les fonctions de frère du mari.
6 Ɗan farin da ta haifa zai ɗauki sunan ɗan’uwan da ya rasu saboda kada sunansa yă ɓace daga Isra’ila.
Le premier-né qu'elle portera succédera au nom de son frère mort, afin que son nom ne soit pas effacé d'Israël.
7 Amma fa, in mutum ba ya so yă auri matar ɗan’uwansa, sai tă tafi wurin dattawa a ƙofar gari tă ce, “Ɗan’uwan mijina ya ƙi yă wanzar da sunan ɗan’uwansa a Isra’ila. Ya ƙi yă cika abin da ya kamaci ɗan’uwan miji yă yi gare ni.”
Si l'homme ne veut pas prendre la femme de son frère, la femme de son frère montera à la porte vers les anciens, et dira: « Le frère de mon mari refuse d'élever à son frère un nom en Israël. Il ne s'acquitte pas envers moi du devoir de frère de mon mari ».
8 Sai dattawan garinsa su kira shi, su kuma yi masa magana. In ya nace yana cewa, “Ba na so in aure ta,”
Alors les anciens de sa ville l'appelleront et lui parleront. S'il se tient debout et dit: « Je ne veux pas la prendre »,
9 sai gwauruwan nan, matar ɗan’uwansa tă haura wurinsa a gaban dattawa, tă tuɓe takalminsa guda, ta tofa masa miyau a fuska, tă ce, “Haka za a yi ga mutumin da zai ƙi kafa gidan ɗan’uwansa.”
la femme de son frère viendra à lui en présence des anciens, détachera sa sandale de son pied et lui crachera au visage. Elle répondra: « Il en sera ainsi de l'homme qui ne bâtit pas la maison de son frère. »
10 Za a kira zuriyarsa a Isra’ila Iyalin da aka tuɓe masa takalmi.
On appellera son nom en Israël: « La maison de celui qui a ôté sa sandale. »
11 In mutane biyu suna faɗa, sai matar mutum ɗaya daga cikinsu ta zo don tă kuɓutar da mijinta daga abokin faɗarsa, ta kuma miƙa hannu ta kama marainan wancan,
Lorsque des hommes se battent entre eux et que la femme de l'un d'eux s'approche pour délivrer son mari de la main de celui qui le frappe, qu'elle étend la main et le saisit par les parties intimes,
12 sai ku yanke hannunta. Kada ku ji tausayinta.
tu lui couperas la main. Ton œil n'aura pas de pitié.
13 Kada ku kasance da ma’auni iri biyu a jakarku, ɗaya babba, ɗaya ƙarami.
Tu n'auras pas dans ton sac des poids différents, un lourd et un léger.
14 Kada ku kasance da mudu iri biyu a jakarku, ɗaya babba, ɗaya ƙarami.
Tu n'auras pas dans ta maison des mesures différentes, une grande et une petite.
15 Dole ku kasance da ma’aunin da kuma mudun da yake daidai, kuma na gaskiya, saboda ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.
Tu auras un poids parfait et juste. Tu auras une mesure parfaite et juste, afin que tes jours se prolongent dans le pays que l'Éternel, ton Dieu, te donne.
16 Gama Ubangiji Allahnku yana ƙyamar duk mai yi waɗannan abubuwa, da kuma mai rashin gaskiya.
Car tous ceux qui font de telles choses, tous ceux qui agissent sans droit, sont en abomination à l'Éternel, ton Dieu.
17 Ku tuna da abin da Amalekawa suka yi muku a hanya, sa’ad da kuka fito Masar.
Souviens-toi de ce qu'Amalek t'a fait en chemin, à ta sortie d'Égypte,
18 Yadda suka yi muku kwanto a hanya, suka fāɗa muku ta baya, suka karkashe waɗanda suka gaji tiɓis. Ba su ko ji tsoron Allah ba.
comment il t'a rencontré en chemin, et a frappé les derniers d'entre vous, tous ceux qui étaient affaiblis derrière toi, quand tu étais faible et fatigué; et il n'a pas craint Dieu.
19 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya ba ku hutu daga dukan abokan gābanku kewaye da ku, a ƙasar da yake ba ku ku mallaka a matsayin gādo, sai ku shafe Amalekawa daga duniya, don kada a ƙara tunawa da su. Kada fa ku manta!
C'est pourquoi, lorsque l'Éternel, ton Dieu, t'aura donné du repos contre tous tes ennemis d'alentour, dans le pays que l'Éternel, ton Dieu, te donne en héritage pour le posséder, tu effaceras de dessous le ciel le souvenir d'Amalek. Tu n'oublieras pas.

< Maimaitawar Shari’a 25 >