< Maimaitawar Shari’a 25 >

1 Idan mūsu ya tashi tsakanin mutum biyu har abin ya kai su kotu, alƙalai kuwa suka yanke hukunci a kan batun, suka kuɓutar da marar laifi sa’an nan suka hukunta mai laifi,
“When there is a strife between men, and they have come near to the judgment, and they have judged, and declared righteous the righteous, and declared wrong the wrongdoer,
2 in mai laifin ya cancanci bulala, alƙali zai sa yă kwanta a yi masa bulala a gabansa da yawan bulalan da ya dace da laifin,
then it has come to pass, if the wrongdoer is to be struck, that the judge has caused him to fall down, and [one] has struck him in his presence, according to the sufficiency of his wrongdoing, by number;
3 amma kada yă yi masa bulala fiye da arba’in. In ya yi masa fiye da haka, za a ƙasƙantar da ɗan’uwanku, zai kuma zama rainanne a idonku.
he strikes him forty [times]; he is not adding, lest he is adding to strike him above these many stripes, and your brother be lightly esteemed in your eyes.
4 Kada ku yi wa saniya takunkumi sa’ad da take tattaka hatsi.
You do not muzzle an ox in its threshing.
5 In’yan’uwa suna zama tare, in ɗayansu ya mutu babu ɗa, kada gwauruwar tă yi aure waje da iyalin. Ɗan’uwan mijinta zai ɗauke ta, yă aure ta, yă kuma cika abin da yă kamaci ɗan’uwan miji yă yi.
When brothers dwell together, and one of them has died and has no son, the wife of the dead is not given to a strange man; her husband’s brother goes in to her, and has taken her to him for a wife, and performs the duty of her husband’s brother;
6 Ɗan farin da ta haifa zai ɗauki sunan ɗan’uwan da ya rasu saboda kada sunansa yă ɓace daga Isra’ila.
and it has been, the firstborn which she bears rises for the name of his dead brother, and his name is not wiped away out of Israel.
7 Amma fa, in mutum ba ya so yă auri matar ɗan’uwansa, sai tă tafi wurin dattawa a ƙofar gari tă ce, “Ɗan’uwan mijina ya ƙi yă wanzar da sunan ɗan’uwansa a Isra’ila. Ya ƙi yă cika abin da ya kamaci ɗan’uwan miji yă yi gare ni.”
And if the man does not delight to take his brother’s wife, then his brother’s wife has gone up to the gate, to the elderly, and said, My husband’s brother is refusing to raise up a name for his brother in Israel; he has not been willing to perform the duty of my husband’s brother;
8 Sai dattawan garinsa su kira shi, su kuma yi masa magana. In ya nace yana cewa, “Ba na so in aure ta,”
and [the] elderly of his city have called for him, and spoken to him, and he has stood and said, I have no desire to take her.
9 sai gwauruwan nan, matar ɗan’uwansa tă haura wurinsa a gaban dattawa, tă tuɓe takalminsa guda, ta tofa masa miyau a fuska, tă ce, “Haka za a yi ga mutumin da zai ƙi kafa gidan ɗan’uwansa.”
Then his brother’s wife has drawn near to him before the eyes of the elderly, and drawn his shoe from off his foot, and spat in his face, and answered and said, Thus it is done to the man who does not build up the house of his brother;
10 Za a kira zuriyarsa a Isra’ila Iyalin da aka tuɓe masa takalmi.
and his name has been called in Israel, The house of him whose shoe is drawn off.
11 In mutane biyu suna faɗa, sai matar mutum ɗaya daga cikinsu ta zo don tă kuɓutar da mijinta daga abokin faɗarsa, ta kuma miƙa hannu ta kama marainan wancan,
When men strive together with one another, and the wife of one has drawn near to deliver her husband out of the hand of his striker, and has put forth her hand, and laid hold on his private parts,
12 sai ku yanke hannunta. Kada ku ji tausayinta.
then you have cut off her hand; your eye does not spare.
13 Kada ku kasance da ma’auni iri biyu a jakarku, ɗaya babba, ɗaya ƙarami.
You do not have [both] a great stone and a small stone in your bag.
14 Kada ku kasance da mudu iri biyu a jakarku, ɗaya babba, ɗaya ƙarami.
You do not have a great ephah and a small ephah in your house.
15 Dole ku kasance da ma’aunin da kuma mudun da yake daidai, kuma na gaskiya, saboda ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.
You have a complete and just stone, [and] you have a complete and just ephah, so that they prolong your days on the ground which your God YHWH is giving to you;
16 Gama Ubangiji Allahnku yana ƙyamar duk mai yi waɗannan abubuwa, da kuma mai rashin gaskiya.
for anyone doing these things, anyone doing iniquity, [is] an abomination [to] your God YHWH.
17 Ku tuna da abin da Amalekawa suka yi muku a hanya, sa’ad da kuka fito Masar.
Remember that which Amalek has done to you in the way in your going out from Egypt,
18 Yadda suka yi muku kwanto a hanya, suka fāɗa muku ta baya, suka karkashe waɗanda suka gaji tiɓis. Ba su ko ji tsoron Allah ba.
that he has met you in the way, and strikes among you all those feeble behind you (when you [were] weary and fatigued), and is not fearing God.
19 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya ba ku hutu daga dukan abokan gābanku kewaye da ku, a ƙasar da yake ba ku ku mallaka a matsayin gādo, sai ku shafe Amalekawa daga duniya, don kada a ƙara tunawa da su. Kada fa ku manta!
And it has been, in your God YHWH giving rest to you from all your surrounding enemies, in the land which your God YHWH is giving to you [for] an inheritance to possess it, you blot out the remembrance of Amalek from under the heavens—you do not forget.”

< Maimaitawar Shari’a 25 >